YA KAMATA MU NEMI AFUWAR SHEIKH DR. AHMAD GUMI

YA KAMATA MU NEMI AFUWAR SHEIKH DR. AHMAD GUMI

A baya can, mun kasance masu kausasa harce idan Sheikh Dr. Ahmad Gumi ya yi magana akan siyasar Nijeriya, a yanzu mun fahimci cewa mun yi kuskure idan muna masa raddi akan abar banza siyasar Nijeriya.


Maganar gaskiya yaki da cin hanci da rashawa a Nijeriya lamari ne mai girma da rikitarwa wanda da wahala ace an kawo karshen cin hanci da rashawa, duk ta'asar da 'dan siyasa zai tabka, da duk irin cin amanar da zai aikata da satar dukiyar al'umma ko da tallafawa ayyukan ta'addanci ne, to yana dawowa cikin jam'iyya mai mulki magana ya kare.

Na taba jin Dr. Ahmad Gumi ya furta wata kalma wanda sai a yanzu ne na fahimci gaskiyar abinda ya furta, yace a batun yaki da cin hanci da rashawa karya ne 'they are all corrupt'. Ma'ana dukkan su maciya rashawa ne.
Duk inda mutum ya kai ga biyewa bangare daya a 'yan siyasar Nijeriya to zai iya kunyata daga karshen al'amari.

Allah Ya sauwake
Daga Datti Assalafiy
Post a Comment (0)
Previous Post Next Post