Namij Baya Kadan By ArewaNow.Com.Ng 1


Zaune suke a parlon cikin hiran jin dad'i
dan yau gidan a cikin nishad'i yake,
Mahmud da yanzu ya shigo cikin miskilanci ya zauna gefen
Mamin shi
tare da tab'e fuska yana ta huci,
ya kalli
Khadija dake gefe rik'e da woya tana mgn daga dukkan alamu da mutumin da ya kora yanzu ne take mgn,
Tana katse kiran ta juyo cikin tsurawa Mahmud d'in ido
da alamun tuhuma ,
Shima idon ya tsura mata tare da katseta cikin had'e fuska yace,
"Wlh ni kunya kike bani ji irin mutanen da suke zuwa suna buga mana layi a k'ofar gida sai kace sun samu gidan mai,
Duk gayyan taru kucen banza".
Ita kuwa harara ta watsa mai cikin bacin rai ta juya ta kalli Mami da Anty dake wurin tace.
" Wlh Mami kuywa yaron nan fad'a ya fita daga idona fisa bilillahi duk Wanda yazo guna sai yai ta koransu ko ni Sa'ar sace ni wlh ban son raini haka jiya yayiwa Sulaiman rashin mutun ci yau kuma ya kori Alh Bashir tome yakeso dani"?.
Shima fuskar ya had'e yana
"Kai da Allah kiyi ta tara tsoffi bayan ba iya rik'e da gsky zasuyi ba ko sun aureki".
Mami ce ta kallesu cikin k'osawa da hali irin nasu dan inda sabon sun saba yanzu suita Sa,insa anjima ajisu suna hira da k'us k'us.
Shiyasa ta mik'e tana "toh kai Mahmud meyasa kake kore mata bak'inta kai wanne irin k'anine wannan".
Anuty ma mi k'ewa tai tana "ke Khadija ya kikeyi har yasan da bak'in naki har ya samu damar koransu"?.
Baki ta tura cikin nunashi da yasa tana
" Wlh Anuty yaron nan ya cika Sa ido ne yaro kamar may"..
Bata kai da rufe bakinta ba ya taso cikin fushi ya tsaya gaban ta yana nunata da yatsa har jikinsa Na bari a fili ake ganin bacin ransa murya Na rawa yace
"Wlh ina gaya miki daina cemin yaro wlh ki kiyayeni waye yaron sai kace wata k'anwar uwata kiyi tace min yaro" a fili b'acin ransa ke bayyana.
"Ehh ancema yaron shekara nawa ne tsaka ninmu ko ka manta Na tunama kana dai sane Nike shiryaku lkcin da kuke zuwa primary ko"?
Had'e fuska yayi tare da matsowa kusa da ita cikin yin k'asa da murya tare da d'an tsura mata ido yana mai lumshesu dayin piki piki dasu yace
" Khadija wlh shi namiji baya kad'an ki dena cemin yaro ko Wai nayi kad'an ni nasan nayi miki yawane ba kad'an ba in kuwa shakku kike Na miki alk'awari gaba zaki gane".
Dariya ta d'anyi cikin rashin d'aukar kala manshi da komai tace
"Wani ba Amman ba kai bakam Dan kana sane ni Anuty kace Amman Dan ka rainani sai kake cemin wani Khadija kai tsaye wlh sai Na had'aka da Abba tukun zaka gane".
Murmushi ya d'anyi tare da cewa
" ai inna ce miki Anuty wlh Na watsa burin raina d'en zan jawowa murad'ina nak'asu".
Mik'ewa tayi tana d'an takawa a hankali hips d'inta Na juyawa cikin rausayawan tace "wlh kai Mahmud ka feye son girma".
Shi kuwa ido ya tsurawa bayan ta tare da sauk'e ajiyar zuciya yana mai lasan lips d'inshi da tuni sun fara bushewa cikin wata iriyar murya yace
" dazu naga wata mai kama dake a bakin to titi komai naku iri d'aya "
Juyowa tayi cikin had'e fuska tace
Mai k'iba ko fara mai hips da yawa ko"?
Ido ya d'an lumshe cikin daga mata gira d'aya yace
"Ya akayi kika san haka take"?
" ai nasan da anga mai irin tsuffata sai ace muna kama ni wlh ban son k'ibar nan".
Shima mik'ewa yayi ya d'an tako ya matsota cikin rada
yace
" ke wlh mace mai k'iba tayi a rayuwata ni banson mace siririya mai zanyi da ramarta mace kam ka samu ko ina ka tab'a bul bul kamar yadda kiken nan ai yafi ko? Ni Sam ban Sha,awar ramammiyiyar mace
Y'ar duma-duma dai tafi wlh".
Matsawa tayi cikin ranta ko mmk take yadda k'anin nata Mahmud bai jin kunyar saki mata irin zantu kannan yaron da mgn ma tsada take mai ko yaushe bai da abokin hira sai littata fanshi da karatu k'ur,ani.
Shi kuwa cikin sanyi yace
"Bacci kike jine"?
Previous Post Next Post