RENONTA ZANYI 1 AND 2 HAUSA NOVEL

Da sunan Allah me rahma me jinkai Allah nakeroko yabani ikon rubuta wannan littafin me suna Renanki~zanyi ya isa gareku kuskuran daxanyi aciki Allah yayafemin Allah yasa littafin ya anfanemu gaba daya @meeen
1⃣
Tafe take akan hanya tana sauri sbd mamanta najiranta da cinikin da akayi susamu su daura abincin dare tana shigowa gidan tundaga xaure tafara kiranta Umma tana daki tafito da hanxari tana cewa Mamana ya akayi kikemin irin wannan kira tace umma nasiyar duka yakare umman tana murmushi tace yawwa yar albarka yanxu ajiye kwanan kije kisiyo mana garin tuwo tace to ta ajiye taxo tatafi taje shagon Danladi tasiyo tana dawowa akan hanyarta se taga wasu maxa su 3 kyawawa amma dayan duk yafisu kyau sede shi ranshi a face yake sauranko sunata firansu tana tahowa harta karaso kusa dashi garin kallansu bata saniba tadan tafashi kadan aiko kamar jira yake ya juyo afusace yana cewa ke wace irin jakace kina tafiya bakya kallan gabanki kawai naji hawaye sun soma xubomin sbd ba'a tafa xagina hakaba kafinma inkai ga magana yajuya gurin abokan tafiyarshi yana ce musu bro's kumukoma gida ba inda xan iya xuwa da wannan kayan tunda wannan akuyar tatafa nan suka faramai magana haba Don aibe baciba kayi hakuri mukarasa kaga mun kusa yace aa shi inba wanka yayi yachanxa kayannan ba baxe jeba suma de ransu yafaci suka juyo Niko inanan atsaye kamar anshukani yana wani yatsina fuska yana cewa kayannan ai sede akonasu Dan baxasu kuma sahuwa ba sukaxo xasu gittani xuciya takuroni bansan sanda nasha gabanshi ba nadaga ledan garin nan naxaxxagemai tunda ga kansa har fuskanshi ai abokannan nashi naganin haka suka xabura suna masu xareacikinsu sbd mamaki nikuma bayan nagama juyemai najuyo na rike hannunshi duka nagoga nawa ajiki sannan. Nacemai yanxu tunda nafada fatar jikinka da tawa sekaje kachanxa wa wawa kawai Wanda besan darajan Dan Adam ba najuya nayi tfy ta alokacin mutane har sun fara taruwa kawai naji anfizgoni

[8:02am, 5/1/2016] Nadear S. Tafida:


2⃣
Najuyo afusace naganshi rike dani yanaso yayimin magana amma tsabar takaici yakasa gashi yakasa bude idanshi daya bude seyaji gari nafixge hannu na najuya natafi shiko yakasa ko motsi se alokacin abokanan tafiyarshi suka lura mutane sun xagayesu se kamatso domin su taimaka mai wasu amutanen nabashi hkr shiko se karamai bakin ciki suke nande daya acikinsu yasa hankacif yana gogemai dayan kuma yana duba inda xasu samu ruwa seya hango wani shago yaje yasiyo yaxubamai yana wankewa yarikeshi dakyar ya iya daga kafarshi idannan nashi yayi jaa kamar barkono suka fara tafiya
**** **** ****
Niko tunda nabar gurin se gabana yafara faduwa sbd ban iya rigima ba nayi mamaki sosai dana iyayimai haka ina tafi INA nadama Lamar nakoma nabashi hkr se kuma natuna xafin dayamin raina ya kuma faci se kuma inna tafadomin arai natuno garin nan fa dashi xamuyi abinci ahakade nakaraso gida ina tunani ina shiga umma tace kindade se kuma takalli hannu na taga ba garin tace ya haka Mamana ba garinne aise nafashe da kuka nace mata garinne yaxube tace garin yaya nace ina tafiya tace to kidena kuka ba rabanmu bane jeki dauko sauran changin kisiyo mana garin kwaki semu jika musha nace to nadauko tace kuyi kinga magriba takawo
***** **** ******
Shiko Don suna xuwa gida be tsaya ko inaba se hanyar bathroom har yakai bakin kofa kuma seya dawo da baya yatsaya bakin kofar yana yamutsa fuska yacire rigar jikinshi da wando Wanda daganinsu yau akafara sasu yarikosu dayatsu biyu yaxo ya huce su Abdul a falo yadaga labile ya watsasu kamar ya watsa Kashi harda shinshina hannu su Abdul de suka kalli juna sukayi murmushi yahucesu yana hararansu yashiga bayi yadinga wanka kamar xe chanxa fata seda yayi ruwa yakai 5 hannun shiko inda tatafa seda yaji yana xafi yana fitowa yasa singlet da 3quarter ya kwanta segasu sun shigo Abdul yace Don pls forget... Tunbe karasa fadaba yadagame hannu yana kallansu da jajayen idanshi yace leave me alone yana gama fadi yajuya musu baya yakwanta kamar me bacci suna fita ya tashi xaune yafadi dakarfi I swear to Almighty sena sa kinyi danasani .....

[8:02am, 5/1/2016] Nadear S. Tafida:
Post a Comment (0)
Previous Post Next Post