Namiji Baya Kadan By ArewaNow.Com.Ng 2


Kai ta Dan gyada mai alamar a a ,
Ajiyar hrt ya sauk'e tare da cewa
Ki hau online akwai lbrin da zan baki"
Karb'ar phone d'in yayi ya bud'e mata data cikin sanyi yace "bari Na tafi d'akinmu
Baby in baki lbri"
yana fita tana binshi a baya ya tana cewa
"Waye babyn kuma "?
Shi dai tafiya yayi yana shak'ar k'amshinta.
Ita kuwa cewa take
" ji yaro da son girma Wai nice babyn lallai ma kuwa Mahmud ka isa".
Shi kuwa yana zuwa d'akin toilet ya fad'a wonka yayi ya zira rigar baccinsa sannan ya kwanta .yana mai jawo woyarshi
K'aninshi Sulaiman ne ya kalleshi cikin tsokona yace .
"Sai chart da Anuty Khadija kuma ko wlh Mahmud ka d'ebo da zafi zan ga ta yadda abinga zai kasance, kai kace babbar mace kakeso ita kuma Anuty Khadija kullum cewa take ita matar manya ce saurayi ko sadaka ta yafe bare kuma kai K'anin bayan ta".
dariya ya danyi cikin sanyi yace rebu da ita, ita bata San cewa namiji bayyin kad'an ko me take so wlh ni Na yadda da kaina Na san zan isar mata nifa ba lusarin na miji bane".
Shi dai Sulaiman ido kawai ya tsura mai yana mmkin yadda Allah ya jarrabi zuciyar d'an uwan nashi da son Yayarta su.
Shiko cikin jin dad'i ya tsurawa picture d'inta na kan dp d'in ta ido yayi ta piki piki da idon cikin hikima ya fara yi mata mgn.
Slm yace da ita tare da cewa
"da forko dai ki cire pic enki Na kan dp d'in ki in ba so kike muyi fad'aba".
Itakowanga ta tura mai tare da cewa
"Nifa Anutyn kace sai ka rink'a abu kamar Kaine babba harda ko mu b'ata to mu bata d'in mana"
dariya yayi tare da cewa "ai ina sonki baby bazan iya b'atawa da keba"
Hmmm tace dashi shi kuwa cikin kuzari da kaifin basira irin nasu Na maza yace.
"Kinsan Ku mata kala kala ne kuna nan tamkar lemun zaki".
cikin dariya da daukar abin as A shi haka yake mai son raha ne tace "toh yaro ya muke"?
Cikin jin zafin Kalmar da take cemai Wai yaro ya d'ago woyar ya kirata
Itako tana gani ta d'aga dan tasan ta cinnashi bai son tace mai yaro.
tana d'agawa
sai jinshi tayi cikin sanyi ya busa mata iska a kunne tare da jan numfashi yace.
" Dan Allah ki dayna cemin yaro ni wlh har ga Allah kina k'ona min rai tunda nasan ni ba yaro bane"
Tab'e fuska tayi tace
"Toh me lbrin da zaka gaya min"?
Jin haka ya sashi k'ara narkewa jikin pillows a ranshi yakeji inama ace a jikinta yake ace gashi gata wlh da sai ya tabbata mata da cewa namiji baya k'aranta fili kuwa cewa yayi
" ko kinsan Ku mata tamkar lemun kuke
Wani lemun zaki ganshi baba a man cikinsa ba komai sai dusa wani kuma ki ganshi k'ara mi Amman cikinsa sai ruwa sai dai kuma sai a samu ruwan ba zak'i wani kuma ki ganshi gashi a cike ga ken fata Amman ba ruwa bare zak'in
Wani kuma zaki ganshi ga kyauwun jiki ga ruwa ga zak'i ga d'an d'ano ga kauda k'ishi da k'ara lfy da Sa kuzari".
Sai kuma yayi shiru ita kuma tunda ya fara mgnar ta tafi tunanin ehh haka nefa wlh maganar sa gsky ce a ranta take cewa wato su maza mu sannan masu ilimin fikk'iwu komai Na mata sun sanshi.
Mgnarsa ce ta katseta cikin kasala yace.
"Toh ke irin wannan lemunne Na k'arshe da na kwatan ta miki"
cikin jin zafin furucin nashi tace
"In kana hasa shenka ka daina sani a ciki yaro Sam baka da kunya".
Murya a dak'ile kamar zai kuka yace
" Dan Allah ki dena cemin yaro wlh zakisa duk randa Na iso gareki Na zalum ceki dan kawar da wannan sunan"
Ita dai bata gane me ya fad'iba bare ta gane ma,anar zancen.
Cikin sanyi dan ta fara jin bacci tace
"Mahmud zanyi bacci"
Ajiyar zuciya ya sauk'e jin dad'i yadda ta kirashi cikin sanyi yace
Toh tashi kike kiyi alwala kizo muyi Addu,ar konciya bacci".
Cikin bacci baccin "tace ai nayi ni tun d'azu "
Cikin rashin sanin zancen zai fito yace "ai nasan kinyi Amman dai alwalan ya worwore yanzu kam".
Previous Post Next Post