RENONTA ZANYI 3 AND 4 HAUSA NOVELS

3⃣
Ya kwanta domin yayi bacci ko xeji sanyi amma bacci ya gagari idanshi daya rufe ido ita yake gani baa tafa hulakantashi irin hakaba yayi danasanin xuwa garin sokoto waishin wanene ma Don Dane ga Alhaji hafix mai dala mahaifinsu yakasance shahararrene shi agarin Kaduna dama wasu dake kewayanta asalinsa mutumin sokotone shima sede basa xumunci yan uwansa hakan yasa yayansa basusan danginsu ba mahaifiyarsa sunanta hajiya falmata yar kasar Sudan ce babanshi ya auro ta shine da babba agurin mahaifinsa bayan anhaifeshi mamanshi tadade bata samu wani cikinba se bayan Don Wanda asalin sunansa Bassam yashiga sec.sch sannan Allah yakawo wani cikin aka haifi kannanshi yan biyu mata daganan kuma se haihuwa tatsaya Don yayi makarantar pri. An sec. Dinsa anan tokish dake Kaduna sannan yayi university dinshi London inda yakaranchi medicine ayanxu haka shi kwararran likitan matane nike name dinshi (Don) yasamo asaline daga abokanan shi yakasance miskiline shi nagaske yaje garin sokoto ne danyin wani aiki shida abokanan Aikinsa kuma abokanansa sunyi kuma ansamu nasara bayan sungama ne se abokinsa Alkasim yace akwai gidan wata gwagganshi anan garin kuma kusan anguwan da akabasu masauki ranan sun shirya kai mata xiyara sbd saura kwana biu sutafi ahanyarsu ta xuwane wannan Abu yasameshi gashi kuma yadau niyyar ramako shin a INA xenemo yar umma ne ? Yananan kwance yana tunani har bacci yadaukeshi
***** **** ******
Washe gari dasafe natashi dahuri Dan nataya ummana aiki kafin lokacin makaranta yayi tatafi bayan nagama shara sena dauki ruwana. Nayi wanka nadauko kayan makaranta na nasa nafito nama ummana sallama tace alabada sa'a nafito lungunmu inata sauri sbd nayi latti ina cikin tafiya senaga daya daga cikin abokansu Wanda nawatsama gari da sauri na isa gurin shi nacemai kai abokin me Dan qaruna yajuyo yana kallanta ta murgudamai bakiabokinka yanxu ya mutu ko kuma anyanke me hannuwa? yayi shiru yana kallanta bata jira amsarshiba tace kafadamai duk randa nakuma haduwa dashi inbeyi wasaba sena ciremai idanshi mekama Dana mujiya kaci saa yanxu makanta xani dase nabika gidanku Nagano gidanku inga yaya fatarshi takoma ya chanxa wata tana kaiwa nan tajuya xata tafi seme tana juyawa tasa idanta cikin nashi turkashi ....

[8:02am, 5/1/2016] Nadear S. Tafida:


4⃣
Ina ganin shi gabanta yafadi amma dake gwanar tsokanace sena fashe da dariya nace Dan karuna yanaganga da hannu dama kyamar taka duk tabanxa ce ina magana ina kara matsowa kusa dashi Dana kawo dap dashi sena danyi baya shiko axuciye ya bude baki da niyyar faramin magana aiko yana budewa ina watsamai miyau aciki jikake kut ya hadiye sbd magana yakesan yi aiko nace kafa menaci banbakiba nahau gudu shima yatake min baya yana bina bakinshi abude nako kara huta gudu nake da iya karfina yana bina har muka kawo islamian mu nakoyi ciki aguje naboye abayan malaminmu segashi yashugo Ashe abokinsama yabiyomu malaminmu yace ke Basma meya faru nakasa magana se haki nake seya juya gurunsu yace bayin Allah me tamuku nasanta da tsokana aiko yadago ido muna hada ido kawai seya fashe da kuka gashi yakasa rufe baki abokinsa naganin haka kawai ya rikeshi suka juya sbd hankalin mutane yadawo Kansu yana rike dashi shiko se waigena yake yana hawaye Niko ina masa gwalogurin xamana kusa da Fatima
***** **** *****
Suna fita Alkasim yakira Abdul yaxo musu da mota sutafi shiko har lokacin ya duka a kasa ya saki baki miyau na dilala kamar wa2 shi kanshi Alkasim inya kalleshi dariya ke xuwamai yanade dannewa Dan karyagane Abdul na xuwa yafito agigice yana tanbayan me yafaru Alkasim yacemai Dan Allah kamashi de musa amota yanxu ba lokacin magana bane kaga mutane na kallanmu suka dagashi yashiga har amotanma dukawa yayi yacigaba da xubar da miyau Abdul dai yana tuki yana waige sbd betafa ganin abokinsu a hali irin haka xe iya cewa be tafa ganin hawayanshi ba Dan shi inranshi yafaci sede kaga idanshi yayi jaa
**** ****** ****
Niko muna tashi nafara bamawa Fatima labarin abinda yafaru tace ke Basma wly ba ruwana wannan fa Dan birni ne suda suna iya kashe mutun inya musu Abu ko sumaka asiri ka haukace hakafa akace sunayi senaji jikina yayi sanyi tsoro ya kamani nace to aibesan gidanmu ba tace ai xe sanine nayi shiru kawai ina tunani
***** ***** *****
Tunda suka shigo gida yashige bayi yafara brush be denaba seda yakarar da macline dinsu duka amma duk da haka yaki yadda da bakin yadauko mouth freshener yadinga fesawa yana fitowa yasauko da akwatinshi yafara hada kayanshi yana gamawa yafito da akwatinsa ahannu atare suka mike suna tanbayarshi lfy dakyar yabude baki yace musu gida xashi sukace habade kayi hkr sauranmu awanni kadan kasan jirgin mune nafarko gobe yadago da jajayan idanshi yace musu wly baxe kara kwana a sokoto ba inba sosuke yamutu ba kawai yajuya ya fita se suka bishi abaya yana fita yahau mota yafigeta aguje ko juyowa beyi ya kallesu ba ......

[8:02am, 5/1/2016] Nadear S. Tafida:
Post a Comment (0)
Previous Post Next Post