'Yan daba sun yi barna a gidan Daso

Tauraruwar fina-finan Hausa, Saratu Gidado, Daso ta bayyana yanda 'yan daba suka kaiwa gidan mijinta dana makwaucinta hari da sanduna da duwatsu, Daso ta ce an lalata musu dukiya me yawa.



Saidai ta kara da cewa basu samu shiga gidajen nasu ba saboda jami'an 'yansanda sun kawo dauki.

Lamarin dai ya farune ranar Litinin din data gabata, muna fatan Allah ya tsare ya kuma mayar da Alheri.

Post a Comment (0)
Previous Post Next Post