Dalilin da yasa na bar Kaduna zuwa Kano _Adam A. Zango

Bayan da wasu daga jihar Kaduna suka bayyana korafinsu a jaridar Leadership kan komawar tauraron fina-finan Hausa kuma mawaki, Adam A. Zango jihar Kano, jarumin ya bayyana dalilinshi na barin jihar.



Ga abonda ya bayyana kamar haka:

'DON ALLAH IDAN KAI BA DAN FIM BANE KADA KA SAKA BAKI DON BATA SHAFI YAN KALLO BA .
NAJI KORAFIN KU YAN KD, KUMA ZAN DAWO KADUNA NANDA WATA UKU BI'IZINILLAH. DAMA RASHIN KUNYA, RASHIN HADIN KAI, RASHIN GIRMAMA NA GABA DA KUMA RASHIN KULAWAN GWAMNATIN KADUNA YASA NA BAR GARIN SABODA NI BANA ZAMA A WURIN DA BABU RESPECT, BABU DOKA, BABU TARBIYYA. SANNAN KUMA NI KADAI BAN ISA IN GYARA HARKAR BA. WANNAN DALILIN YASA NA BAR KADUNA NA KOMA KANO SANNAN A KANON MA BABU WANDA YAKE GANINA IDAN BA A WURIN AIKI BA KO KUMA WURIN WANI TARO SABODA KANON MA YANZU DUK HAKAN TAKE KOMAI YA LALACE SABODA RASHIN TARBIYYAR KASHI 80 DAGA CIKINMU YAN FILM WANDA A BAYA BA HAKA MUKE BA.

MAGANATA BATA SHAFI AL'UMMAR KANO DA KADUNA BA (MA'ANA YAN KALLO)__DA YAN UWANA YAN FIM KAWAI NAKEYI. KUMA DUK MAI KYAKYKYAWAR ZUCIYA YA SAN A CIKIN MU YA SAN GASKIYA.'

1 Comments

  1. Kai kayi zaman ka a kano zai fima. Kano akwai kaya everything

    ReplyDelete
Post a Comment
Previous Post Next Post