a kasar Nigeria aka haifeni-Atiku ya gayawa y'an adawa

                                 atiku
Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar PDP,Atiku Abubakar ya mayarwa jam'iyyar APC martani akan cewa da suka yi asalinshi ba dan Najeriya bane, Atiku yace a Najeriya aka haifeshi.
A wata sanarwa da ya fitar Atiku yace an haifeshi a November 25, 1946, a Jada dake jihar Adamawa kuma mahaifinshi, Garba Atiku Abdulkadir dan asalin jihar Sakkwato ne sannan mahaifiyarshi, A'isha Kande 'yar Asalin jihar Jigawace dan haka shi dan Najeriyane kuma ya cancanci yin takarar shugaban kasa.
Post a Comment (0)
Previous Post Next Post