Shugaba Buhari ya yabawa Osinbajo bisa ci gaba da aikin da ya kaishi Kogi duk da hadarin jirgin sama da ya faru dashi

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya yabawa mataimakinshi, Farfesa Yemi Osinbajo wanda duk da hadarin jirgin da yayi amma hakan bai hanashi ci gaba da aikin da ya kaishi jihar Kogi ba.



Shugaban ya kira Osinbajo a waya inda ya yabamai sosai akan jajircewa da ya nuna bayan jirgin saman da yake kai yayi hadari, yace firgicin hadarin be kama kaba haka ka ci gaba da aikin da ya kaika Kogi wannan ya nuna iri n yanda kake son bautawa kasa ba tare da nuna gajiyawaba.

Ina yaba maka kai da sauran abokan tafiyarka, kamar yanda yake kunshe a cikin sanarwar da Garba shehu ya fitar.

Post a Comment (0)
Previous Post Next Post