Jawabin Mai martaba Sarkin Kano akan Shigar Malamai Siyasa

Mai Martaba Sarkin Kano Muhammad Sanusi II Yayi Bayani Mai Muhimmanci.

Ba’a Hana Mutum Ra’ayi Ba, Kowa Yana da Ra’ayinsa, Amman Kada Ku Shigar Da Kanku Cikin Siyasa. Malamai Su Hau Kan Mumbari ko Hakimai su Tara Jama’a Ace A Zabi Wanannan Jam’iyya Ko Waccan Ba Aikinmu Bane.


Ka Futo Akan Mumbari Ko Gidan Radio Ko Gidan Talabijin Shi Ne Ya Kawo Malamai Suna magana ‘yan siyasa suna Magana, Martabar Da Allah Yayi Muku Na Malamai Da Sarautar Nan Kada Mu Ringa Shigar Da Ita Inda Wani Zai Zage mu, Koya Shiga Cikin Mutuncinku Wannan fagen su ne.

Kwanakin Can Baya Munyi Magana Mukace In Za’a Zabi Shugabanni A Zabi Mai Ilimi, ‘Yan Jarida Sukace Sarkin Kano Yace Kar A Zabi Wani Dan Takara Don Bashi Da Certificate, Ni Ban San Maganar Certificate Ba Kuma Maganar Ilimi Nayi.

Sannan Mai Martaba Sarki Ya Ja Hankalin ‘Yan Siyasa Dangane da Haifar Da Sara Da Suka A Yayin Kamfen, Da Kuma Munanan Kalamai Da ‘Yan Siyasa Keyi, Indai Sarkin Yace Wannan Ba Komai Bane Sai Warware Addu’o’in Zaman Lafiya Da Sarkin Ke Jagoranta.

Sannan Ya Nemi Da A Gurfanar Da Duk ‘Yan Siyasar Da Sukayi Kira Kan A Zubda Jinin Al’umma A Gaban Hukuma. A Karshe Mai Martaba Sarkin Yayi Jan Hankali Sosai Dangane Da Wannan Zabe Dake Karatomu. Ubangiji Allah Ya Karawa Sarki Ingantacciyar Lafiya Da Nisan Kwana Mai Amfani. Ameen.
Post a Comment (0)
Previous Post Next Post