Rahama Sadau ta kamu da soyayya: Karanta zafafan kalaman soyayya da ta gayawa saurayinta

Rahama Sadau ta kamu da soyayya: Karanta zafafan kalaman soyayya da ta gayawa saurayinta

Da alama tauraruwar fina-finan Hausa da turanci,Rahama Sadau ta kamu da soyayyar saurayinta sosai, a makon da ya gabatane ta bayyana cewa gata baki harkunne saboda zata sake ganinshi.



A wannan karin kuma Rahamar ta fitone ta dandalinta na sada zumunta inda ta fadi wasu kalaman soyayya ga saurayin nata duk da dai har yanzu bata bayyana ko wanene ba.

Rahama ta rubuta cewa, abin akwai ban mamaki irin yanda muke kamuwa da soyayyar wanda bamu yi tsammani ba a kuma lokacin da ba muyi tsammani ba. Tace mai kaine haskena a cikin Duhu.

Ta kara da cewa ba lallai ta iya gayawa Duniya irin soyayyar da take mishi ba amma tasan cewa shi ya sani, zasu kasance tare har abada.


Post a Comment (0)
Previous Post Next Post