Khadija Bukar Abba Ta Yi Murabus Daga Mukamninta Na Minista
Uwargidan tsohon gwamnan jihar Yobe Hajiya Khadija Bukar Abba Ibrahim ta
yi murabus daga kujerarta na karamar ministan harkokin kasashen waje na
Nijeriya.
Jaridar Punch ta ruwaito cewar, Hajiya Khadija ta yi murabus ne domin
shiga zaben majalisar wakilai da za a gudanar ranar 16 ga watan
Feburairun 2019 a karkashin tutar jam'iyyar APC.
Daga Haji Shehu