ZA'A GURFANAR DA 'YAN MADIGO A KUTUN MUSULUNCI A JIHAR KANO

 
Mataimakin kwamandan Hisbah na jihar Isa Sani ya shaida wa BBC cewa sauran wadanda za a kai kotun sun hada da mutane 10 wadanda suka halarci wurin da aka shirya bikin, da kuma wanda ya bayar da hayar gidan da aka shirya bikin.
A ranar Litini ce hukumar ta damke matan a unguwar Sabon Garin Kano, kuma har yanzu hukmar na rike da guda biyu daga cikin su.

Mai magana da yawun kotun shari'a ta Kano, Baba Jibo Ibrahim ya ce suna sane da mmaganar sannan su na jiran hukumar Hisbah ta kawo maganar gaban kotun domin a fara sauraron karar.
Hukumar Hisbah ta ce za ta tuhumi matan ne da aikata rashin da'a, kasancewar ta kama su ne kafin a daura auren.
Dokar Najeriya dai ta haramta auren jinsi guda, kuma duk wanda aka kama da laifin zai iya kwashe kimanin shekara 14 a gidan yari.
Post a Comment (0)
Previous Post Next Post