Sani Danja Da Matar Sa Mansura Isah Sun Ba Mara Da Kunya

Tabbas, Sani Danja da Mansura Isah sun ba Mara 'da kunya. Domin sun yi abinda ba'a taba zaton zasu yi ba.Ko da yake wasu hangen nesa sun gano hakan zata iya faruwa. Ina magana ne akan auren da suka yi tun shekarun baya. Wasu suna ganin kamar auren ba zai jima ba za'a rabu. Said kuma ga shi Allah ya yi ikonsa har yanzu suna tare.

Abin burgewa shine yanda kullum su kara son juna. Duk da 'yayayen da suka tara bai hanasu soyayya ba. Suna Son junansu.

Ranar da akayi murnar shagayowar ranar da aka haifi Junior Yakubu Sani Musa Danja, a ranar duk wanda yaga Danja da Mansura Isah sai ya tabbatar suna son juna.

Wannan ma ya is a hujja ga masu zargin 'yan fim basa auren 'yar fim. Sabida tanbadewa da suke yi tun adatsa. Wannan Sani Musa Danja da Mansura Isah ya tabbatar mana ba haka bane.

Domin idan da hakane da Danja bai auri Mansura ba, kuma da Marigayi Ahmed S Nuhu da bai auri Hafsat Shehu ba.
Akwai 'yan fim mata masu tarin yawa wanda suka Auri 'yan fim kuma har yanzu suna tare.

Dan haka muna yiwa Maigida masharin kukan mu Sani Musa Danja da matar Anty Mansura mai kula da bukarmu ta kaiwa maigidanmu ubangidan mu Danja da ya share mana hawaye fatan alkairi, Allah yasa mutuwace zata raba.

Post a Comment (0)
Previous Post Next Post