Cikakken Sakon Tsohuwar Jaruma Fim Ummi Zeezee Zuwa Ga Yan Nigeria

Ga Sakon Tsohuwar Jarumar Fim Ummi Zeezee Zuwa Ga Yan Nigeria Ta Rubuta Wannan Sakon A Shafin Instagram Dinta

""Salam dear nigerians ,wasu suna amfani da sunana a face book sunamin karya iri iri da kuma bata suna a gareni Wanda ina kyautata zaton masoyan APC ne.hakan ya samo asaline domin sunsan bana shiri da boss dinsu Mr president.last week sun hada hotona Dana wani gardin banza a daji wai yana lalata dani sukaga hoton baiyi tasiri ba domin Allah ba azzalumin bawansa bane baya kuma kama bawa da laifin da bai aikata ba.to da suka ga hotona da suka hada da gardi Wanda kuke cewa timaya ne baiyi tasiri ba sai kuma suka dawo suka ce wai ni yar shi'A ce,shima suka ga baiyi tasiri ba da suka dangan tani da shi'A.sai kuma yau suka sake cewa wai na fita daga shi'A har na dawo ina addu'a Allah ya dauwa Mar da "sir zazzaky " a gidan yari .to karya ake min ni Sam banyi maganah akan sir zazzaky cewar Allah ya dauwa Mar dashi a gidan yari ba domin ni ina tsananin girmama sir zazzaky saboda sunansa daya Dana mahaifina kuma ni aduniya duk mai sunan mahaifina to ina daraji shi saboda duk mai sunan kallon uba nake masa a sakamakon kaunar da nakewa babana sosai.dan haka karya akemin .

Kuma ku masu son batamin suna ina son ku sani cewa annabi Muhammad s.a.w.yace :in duniya zata taru bata ISA ta daurawa bawa abunda Allah bai dauramasa ba na masifa ko alkairi haka kuma yace in da duniya zata taru bata ISA ta daukewa bawa abunda Allah ya daurawa bawansa na masifa ko alkairi.dan haka na dogara ga Allah kuma zai kare ni a bisa sharrin da kukemin iri iri akan buhari.sannan naji kunce na tuba wai na dena adawa da buhari ko ?to shima karya kukemin.ni yanzu ma na fara adawa dashi indai akan siyasa ne ,nagode.

daga ummi ibrahim(zeezee)""

Post a Comment (0)
Previous Post Next Post