Babu Jarumar Kannywood Da Zata Iya Fice Kamar Rahma Sadau

Babu Jarumar Kannywood Da Zata Iya Fice Kamar  Rahma Sadau

Rahama Sadau wata Jaruma ce a kasar Najeriya wadda tayi fice wajen a fannin wasan kwaikwayo na masana’antar Kannywood. An haifi Sadau a ranar 7 da watan Disamba na shekara ta alif dari tara da casa’in da uku (7 December 1993) a unguwar Sarki dake cikin garin Kaduna na Jihar ta Kaduna a Najeriya.

Ta shiga masana’antar Kannywood a shekarar 2013. Sadau ta kasance daya tilo wajen tafka mahawara a cikin yaren Hausa, Turanci da Indiyanci baki daya. Jaruma Sadau ta samu fice bayan fitowar ta a wani shiri mai suna “Gani Ga Wane” tare da Jarumi Ali Nuhu.

Duk da dai cewar Jaruma Rahama Sadau ta samu fice a ita masana’antar ta Kannywood, sai dai kuma a ranar 2 ga watan Oktoba na wannan shekata ta dubu biyu da sha shida (2 October 2016) kungiyar MOPPAN ta samu dakatar da Jarumar kasancewar samunta da laifin rungumar wani mawaqi a wani faifan bidiyo mai suna ClassiQ wanda ya fito daga yankin Jos na jihar Filato a Najeriya. Ita dai wannan dakatarwa bata samu cirewa ba har a yanzu inda wadansu kan kalle ta a matsayin kora gaba daya daga cikin masana’antar.

Kungiyar MOPPAN tayi tsokaci da cewar rungumar da Jarumar tayi ya saba tarbiya da tsari irin na duk wani mai yin shirin fim na Hausa. Sai dai korar Jaruma Rahama Sadau bai hana fina finai masu hoton ta fita ba duk da cewar masu wallafa shirin na fina finan basu ci gaba da sakata ba a cikin shirin sabbin fina finai. Hakan kuwa tana faruwa ne sakamakon cewar akwai fina finai da dama wadanda Jaruma Sadau take cikin su da basu samu fita ba a kasuwannin fina finai a lokacin da akayi kata ita waccan kora.

Duk Da Hakan Kamfanin Google Suna Nuna Cewa Anfi Duba Labarin Rahma Sadau Fiye Da Sauran Jaruman A Lokacin Da Majiyarmu Ta Duba.

Hakan Yasa Jarumar Ta Samu Kyautuka Da Da-ma  Daga Kamfani Da Kuma Masu Bada Award Wasu Sunce Mah Korarta Kannywood Albarka CE Agareta Domin Ya Kawo Mata cigaba Ciki Sauri Fiye Da Sauran Jarumai Mata Na Kannywood.

Akwai Manyan Mata Irin Su Hadiza Gabon,Nafisa Abdullahi Wanda Sunfi Ta Dadewa Amma Ta Kera Su Wajan Fice Duk Da Yanzu Suma Sun Koma Fim Din Kudancin Nijeriya.

Rahma Sadau Yanzu Na Koma Abun Koyi Ga Manyan Mata A Arewacin Nijeriya Inda Manyan Gidan Jarida Na Leadership Sun Kira Sunanta Amatsayin Jaruma Mai Jarumta Da Kuma Gwazo Inda Har Ta Samu Kyautar babbar jaruma ta Kannywood.

Wasu Suna Ganin Cewa Ilmin Ta Shine Ya Taimake ta Sosai Wajan Kara Kaita Sama Sosai.

Post a Comment (0)
Previous Post Next Post