Wani malamin addini ya bayyana cewa shugaba Buhari zai mutu kamin zabe
Me kare muradin gwamnatin shugaban kasa musamman a shafukan sada
zumunta, Kayode Ogundamisi ya saka wani fasto daga kasar Afrika ta Kudu
da yayi kintacen cewa shugaba Buhari ba zai kai lokacin zabe ba sannan
ya mayarmai da martani.
Fasto me suna Samuel Akinbodunse ya bayyana cewa, Allah ya gayamai
shugaban kasa, Muhammadu Buhari ba zai kai lokacin zabe ba, mutuwa zai
yi.
Kayode yace, dan Allah menene sunan wannan faston?
zan so ace bayan kintacen mutuwar shugaba Buhari fastoci zasu rika kuma
kintacen mutuwar shuwagabannin kungiyar Boko Haram, da alama Allahn da
suke bautawa yana mancewa ne irin wadancan mutane.