Sakonni zamu turawa mutane: Bazan yi amfani da kudin gwamnati wajan yakin neman zabe ba>>Buhari
Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya bayyana cewa ba zai taba bari a taba
asusun gwamnati ba dan daukar kudi a mishi yakin neman zabe ba.
Buhari ya bayyana hakane ta hannun me magana da yawunshi, Malam Garba Shehu bayan kammala taron majalisar koli jiya, Laraba.
Ya bayyana cewa a yi amfani da sakon wayar hannu da sauran kafafen sada
zumunta dan neman kuri'un 'yan Najeriya, ni bazan fitar da kudi dan a
baiwa mutane su zabemu ba, injishi.
Yace 'yan Najeriya na bukatar canji, dan haka an daina siyasar bayar da kudi ga masu zabe dan su zabi dan takara.