HAUSA NOVEL:NI DA FAUZAN COMPLETE

NI DA YAH FAUZAN 1 to 90

<i>[01/07, 12:03 a.m.] ‪+234 706 571 7620‬: Ya🔅💜🔅                  🔅💜🔅
      🔅                             🔅
      *NIDA YAH FAUZAN*

                🔆💚🔆
                      🔆
🔆💙🔆                 🔆💙🔆
     🔆  love story 💋    🔆
Zakuga na canza sunan novel daga a duniyar nan ya koma nida yah fauzan
       Amma fah duk story din daya ne

    Ohh my gym we already meet again Thanks god, yah allah protect me from evil people🙏😄


I really love you my sisters phateemerh
Asma'u
Khadeejerh
Hauwa'u
Aysha
Bilkisu
Ibraheem

   I didnt forget you sisters mariya aisha hafsat we together forever💋

I really love you
Mother nd father😘

You are the only one a i love in my life my........

How can i forget you my friend rahma auwal muhammad we are together💋


My cousins i love you too😉


I cant forget you in my life aliyu ahmad sa'i and sadiya soja gayu i really miss you may your soul rest in peace😭😭😭😭😭

Bissmillahir rahmanu raheem,

Kuka takeyi sosai cikin mota dan bata masan abinda ke faruwa da ita ba, ji takeyi duniya ta mata zafi
       Kiran da aka karayi mata ne ya dawo da ita cikin hankalinta dauka tayi bansan me akace mata ba naji tace ganin zuwa tasake fashewa da kuka
     Bakin wani babban asibiti sukayi parking tafito da gudu tashiga ciki, wani daki ta bud'e tashiga inda tayi karo da gawar mutum biyu kwance an rufesu da farin kyalle
     Kuka tasake fashewa dashi ta duka kasa kusa da gawar tana kuka bude daya daga ciki tayi taga abinda ya kara tada mata hankali
    Ihun da tayi ne yasa masu aikin asibitin suka rugo da gudu suka riketa numfashinta ya dauke nan ta suma
     Nurse ce ta daurata kan gado ta nufi wani sashe da ita, wani babban mutum ne mai kudin gaske ya shigo asibitin yana tambayar dakin da aka kai gawar engineer jafar da matarsa
       Nuna mashi akayi ya nufi wurin ya shiga duk kokarin da yayi na danne hawayenshi kasawa yayi sai da yayi hawaye'
        Fitowa yayi yana share hawaye office din doctor din dake rike da gawar yaje ya nemi abashi su za'ayi zana ida, an kau bashi su din cikin ikon allah akayi masu wanka aka rufesu(allah yasa mucika da imani)
    Karfe 8:00pm bayan ya koma gida doctor dinnan ya bugo mashi ya sanar dashi cewa gafa yar wanda ya rasunan a asbiti ana kula da ita dan fad'uwa tayi sadda taga gawar
     Yace toh shikenan aci gaba da kula da ita gobe da safe zaizo nan din,
    *Washe gari* tunda safe wajen 9:00 ya nufi asibitin aka kaishi dakin da yarinyar take, kwance take da alama bacci take amma hawaye nata bin gefan fuskarta, kuma ga dukkan alamu bajin dadi baccin takeyi ba
    Tausayinta ya kamashi har sai da yayi hawaye, cikin baccin banda innalilahi ba abinda take furtawa
    Fitowa yayi da dakin ya nufi office din doctor din dake kula da ita, doctor ya gaya mashi cewa zata farka bada dadewa ba dan yanzu ma allura bacci akayi mata
     Sunyi da doctor din zai dawo anjima ya dauketa dan zasu salleme ta
   Daga nan gidan alhaji jafar ya wuce suna amsar gaisuwa

*DIDECATED TO YOU Asmie b aliyu*💋💋💋

 *mamy da abdul sunce agaishe daku*😄😄😄😄
Love you all my fans💋💋💋💋

*COMING SOON AFTER SALLAH*

*IDan kunaso inyi shi sai kuyi mani coment ta number da zan rubuta akasa, dama inaso in sanar daku wasu suna tunanin cewa number da nake rubutawa tawace toh bani bace inasa number friends dina ne*

*+12308033256478*
*+12308145186542*

Idan har nasamu 50 coment toh zanyi novel din
[01/07, 12:03 a.m.] ‪+234 706 571 7620‬: Ya🔅💜🔅              🔅💜🔅
      🔅                         🔅
       
       *NIDA YAH FAUZAN*              🔆💙🔆                🔆💙🔆
      🔆 love story💋    🔆

Ooh god protect me from evil people

Episode 6-10

      Karfe hud'u da marece driver yaje ya dauko yarinyar nan dake asibiti, gidansu aka kaita inda taga taron mutane anata zaman gaisuwa
     Idanta cike da kwalla tafito inda mutane suke taje ta durkusa kasa tana gaishe su" kowa hakuri yake bata amma  barrister yayi shiru yana kallanta
    Mikewa tayi tashiga ciki inda bata ga kowa ba sai masu aikin gidansu, kan kujera ta fad'a tana kuka
     Haka akaita zaman gaisuwa har aka kwana bakwai

*Asalin labarin*  
Wacece wannan yarinya?
Sunanta rukaqyya amma iyayenta na kiranta da annah, Mahaifinta dan asalin garin nijar ne aiki ya kawoshi nan
        Wata rana yaje aiki gana acan ne ya gano mahaifiyar annah ya aurota, annah batasan kowa nata ba sbd tun tana karama ake zuwa gana da ita, bayan tafara karatu kuma aka bar zuwa da ita
     Haka dangin babanta tana karama taje batasan kowa ba, kuma bata ta'ba ganin wani yazo ba yanzu shekararta 16 kenan, sunan mahaifinta engineer jafar,mahaifiyarta kuma ruqayya sunanta annah taci
    Iyayen annah sun mutu sana diyar had'arin jirgi kuma ita kadai allah ya basu, sunbar mata dukiya mai yawan gaske

Waye barrister umar adoro?
Shine babban aminin alhaji jafar sun dade tare, mutum wane me halin kirki ga kamala yana da yara 4 babban danshi shine fauzan,halimatu(leemas),aminatu(ummi),khadeeja(deejah)
     Fauzan yana da shekara 25 yanzu yana can london ya gama karatunshi na doctor,su kuma yan matan suna gida suna jiran admission zasu fara zuwa universty
       Leemas shekararta 17 Deejah kuma 16 ummi kuma 15 amma duk kansu d'aya

Annah na zaune falo ita da masu aikin gidan tayi tagumi barrister umar ya shigo da sauri tamike ta gaishe yayi dan murmushi yace lfy qlau yata
    Zama yayi tayi shiru ya kalleta yace annah kinsan dai ya muke da mahaifinki koh? Tace eh
     Yace yawwa annah ke yarinya ce karama wadda baki isa abarki ki zauna gidannan kedai ba
      Mutane zasuyi ta kawo maki hari saka makon dukiyar da aka bar maki
    Dan haka kishirya yanzu ki dauko kayanki zantafi dake gidana ki zauna tare da yayana, ta danyi shiru sannan tace abba naji abinda kace amma idan ina nan zanfi samun kwanciyar hankali abba
    Sbd zan ringa ganin inda nayi rayuwa tare da iyayena,yayi murmushi yace annah hakuri zakiyi mutafi zamanki bazai yuwu ba
     Haka annah ta share hawayenta tamike ta shiga ciki ta kwaso kayanta akwati 5 masu aikin ne suka kai matasu cikin mota,
     Hotan ta dasu kayi ita da iyayenta ta dauko tarike ahannu tana kuka
    Wani babban gida suka shiga wanda zagaye yake da yan sanda,sukayi parking da gudu masu aikin gidan suka taho boot aka bud'e suka kwashi akwatuna suka shiga dasu ciki
    Barrister ya kira daya daga cikin masu aikin yace ya shiga da annah ciki ya kaita wurin hajiya(matarshi) yace ga yarinyar nan, ya kalli annah yace zanje office idan nadawo zamuyi mgn game da dukiyarki,tace toh
     Ciki aka shiga da ita inda taga wasu yan mata a falon su uku sunata kallo a tv, d'aga kai tayi taci karo da hotan wani saurayi handsome fari ne tas gashi da manyan idanu ya danyi murmushi dimple din fuskarshi ya kara mashi kyau, sanye yake da fararen kaya da alama doctor ne
     Ida shigowa tayi masu aikin suka gama aje kayan sukace yawwa ga bakuwa alhaji yace ashigo da ita
     Babu wadda ta kalleta sai d'aya daga ciki tamike tayi dan murmushi tace sannu da zuwa
     Tace yawwa, yarinyar tace zauna mana annah ta zauna, ta kalli annah tace sunana leemas kefa? Tace annah
    Sauran suka d'ago suka kalli juna suka kwashe da dariya


DIDECATED TO YOU *Asmie b aliyu*💋💋💋


Love you all my fans💋💋💋💋
[01/07, 12:03 a.m.] ‪+234 706 571 7620‬: Ya🔆💜🔆               🔆💜🔆
      🔆                          🔆

      *NIDA YAH FAUZAN*

🔆💙🔆                   🔆💙🔆
      🔆                             🔆


*Episode 11-15*

Written by
*Maryerm mukhtar*

Leemas bataji dadin abinda yan uwanta sukayi ba ta danyi murmushi tace annah ya hakuri"tace alhamdulilahi leemas takara da cewa allah ya gafarta masu
      Shigowar ummansu ce ta katse ta,leemas tace umma ga annah tazo wadda dady yace zata dawo nan gidan
     Umma tayi murmushi tace sannu annah allah ya kara maki hakuri da juriya, tace ameen aunty nagode
     Umma tace ki kaita dakin deejah tare zasu ringa kwana kinga keda ummi daki d'aya deejah kuma ita da annah
     Deejah har ta bud'e baki zatayi mgn taga umma ta watsa mata harara yasa tayi shiru
     Dakin kau aka kaita dan madaidaici dan harda toilet ciki ga tv da sauran kayan kallon,masu aikin cikin gidan mata su suka shigar da kayan annah leemas ta tayata suka jera kayan cikin wadrop
     Da yake da bare daya deejah ke amfani, zama kan gado annah tayi tabuga tagumi leemas tace annah hakuri zakiyi addu'a kawai suke bukata wurinki
     Annah tace nagode leemas dan yanzu inaji a jikina nasamu yar uwa dan dama na dade ina neman wadda zan ringa shawar warina da ita
     Leemas tace yanzu bari insa akawo maki lemu kisha koh, annah tace a'a na koshi wlh kibari sai anjima bacci nakeji yanzu jiya banyi bacci ba, leemas tace toh ki kwanta idan kintashi sai muyi lbr mai dadi
      Kwanciya tayi leemas kuma tafita tarufe mata kofar, har karfe 12:00 annah na bacci sai wajen 1:30 ta tashi tayi sallah ta dade tana addu'a mikewa tayi tafito falo ta Hango su can bisa dining table suna cin abinci su uku
       Leemas ce tayi mata alamar ta idaso da kyar ta iya matswa sbd kallon da taga sauran biyun suna mata, leemas taja kujera tace ta zauna
    Bayan ta zauna ne leemas ta zuba mata shinkafa da miya taji kaji sosai leemas tace dan allah annah kici karkj barshi kinji tace toh
      Da kyar ta iya cin spoon7 tace takoshi leemas tace anya kuwa, annah tace wlh na koshi ne
     Leemas tace toh ga drinks nan wane kikeso?annah tace nafison lacasera leemas tace kice ra'ayinku d'aya da yah fauzan shima duk yafi sonta, annah tai murmushi miko mata ita tayi
    Tafara sha ko rabi batayi ba itama ta aje, suna gama cin abinci leemas tajata suka tafi can dwonsteps karamin falonsu dake kasa ta kunna masu kallo sunayi
    Da la'asar bayan sungama sallah annah tashiga toilet tayi wanka tasa riga da skirt na atamfa sunmata kyau sosai sai dai daka ganta kasan tarame sbd yanda kayan sukaso suyi mata yawa
       Abayarta ta maida leemas tace tazo suje garden suyi fira acan, tunda sukaje basu dawo ba sai magriba sadda suka shigo gida masu aiki nata shirya dinner akan table
       Ciki suka shiga sukayi sallah sannan tafito falo dinning kowa ya zauna aka fara zubama kowa abinci,anzo zubama annah tace a'a ita bata cin abinci da daddare sai dai freshmilk da cake abinci ya mata nauyi da daddare
    Leemas tasa aka dauko mata freshmilk din da cake taci


DiDECATED TO YOU *Asmie b aliyu*💋💋💋

Maryerm mukhtar👅👅👅👅👅👅👅
   
Love you al my fans💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽
[01/07, 12:03 a.m.] ‪+234 706 571 7620‬: Ya🔆💜🔆               🔆💜🔆
     🔆                          🔆

    *NIDA YAH FAUZAN*
🔆💙🔆                  🔆💙🔆
     🔆                             🔆

*writeen by Maryam mukhtar*


*Episode 16-20*

Writeen by
*Maryerm Mukhtar*

Da daddaren wajen 9:00 kowa yaje ya kwanta annah tanufi dakin tana shiga ta tadda deejah tayi bacci kuma gashi takashe fitila,  annah bata iya bacci cikin duhu da fitila take kwana dan ko sadda tana gida haka take
     kunna fitila tayi deejah ta farko wani kallo ta watsa ma annah tare da cewa dallah malama miye zaki kunna manu fitila idan zaki kwanta ki kwanta danni bacci nikeji
    Annah tace deejah bana iya bacci cikin duhu dan allah kibarni in kwanta da fitila"tsoki deejah tayi ta kashe fitilar ta kwanta,  ranar sai dai falo annah ta kwana

*washe gari*
Basu tashi ba sai karfe 10:00  leemas tazo ta tadda annah a falo leemas tace annah nan kika kwana??annah tace eh leemas tace sbd me hala deejah ta hanaki zama lfy koh?annah tace a'a wlh ban iya kwana fitila kashe shiyasa nadawo falo na kwanta
    leemas tace toh shikenan bari ummi zata koma dakin nidake sai mu ringa kwana tare kinji,  annah tace toh nagode
    Kitchen sukaje tare suka had'a breakfast komi suka ajeshi bisa dinning sannan suka koma dakin su leemas annah tayi wanka tasa kaya falo sukafito sukayi breakfast  deejah sai harare harare sukeyi
    bayan sun dawo falo Momy ke cewa yawwa gobe zakuga wani babban suprise zakuyi mamaki fah,  ummi tace Momy miye suprise din?Momy  tace A'a sai dai gobe kungani da kanku
     deejah tai dariya tace uhmm momy nasan ko miye dan naji kina waya da suprise din"momy tace Ooh dai koma miye sai goben kunji
   Annah dai jinsu kawai takeyi sbd jikinta yayi sanyi dasu deejah,  momy tace babanku yace zai kawo wani bako gobe kuma dakin fauzan zai ajeshi dan haka leemas kuje ku gyera keda ummi" ummi tace momy wlh cikina ciwo suje ita da deejah mana
     annah tace bari muje nida leemas din mu gyera,  mikewa sukayi sukaje dakin suna budewa pic din fauzan annah taci karo dashi sanye cikin black kaya
    wani irin kwarjini yayi mata ta tsaya tana kallan pic din, annah tace leemas waye wannan? leemas tace yah fauzan ne shine babba nan gidan dagashi sai ni sai ummi da deejah
    annah tace amma fa yana da kyau sosai"leemas tace sai ma idan kinganshi fili yafi haka kyau sai dai ya ciki iya yi
    mata da yawa nasanshi amma baya kulasu yanada fad'a sosai bayasan karya kuma yanasan mutum mai gaskiya amma fah yana da girman kai sosai dan zai iya ganinki ya dauke kai koda ya sanki
      Annah tace tab lallai yana da matsala gashi kuwa ni ya min ammah fa afuska halinshi baimin ba gsky"leemas tace ba ke kadai kikace haka ba duk kawayen mu dasuka ganshi sun fadi haka
     Annah tace mufara aikinmu goge goge suka fara annah ta jawo wata wadrope taga papers sun fado da yawa da alama letters ne,  budewa tayi taga da alama mace ce yayi mawa kalaman ciki sun burgeta sosai ta maida tacigaba da aikinta
     wani labule ta zage ban taci karo da pic din wata budurwa black beauty mai kyau,  annah tace wacece wannan??leemas tace wannan *safiyya ce*

This is just the beginning


DIDECATED TO YOU *Asmie b aliyu*💋💋💋


Maryerm mukhtar👅👅👅👅👅👅👅

Love you all my fans
[01/07, 12:03 a.m.] ‪+234 706 571 7620‬: YaYa🔆💜🔆               🔆💜🔆
     🔆                          🔆
  *NIDA YAH FAUZAN*
🔆💙🔆                🔆💙🔆
      🔆                          🔆


*Episode 26-30*

*MARYERM MUKHTAR HAUSA NOVELS GROUPS*📚📖📘✍🏼


✍🏼Written by
Maryerm mukhtar

Leemas tace yaya bari inkirta ku gaisa mana tana ciki"yace a'a kyaleta zan ganta ne tunda cikin gidannan take,
   *washe gari*
karfe 10:00  suka tashi daga bacci leemas da annah again sukayi breakfast a ranar,  wanka sukaje sukayi annah tasa riga da skirt na tamfa blue,  tayi mata kyau sosai abinka da farin mutum
    Falo sukafito suna zazzaune kan dinning zasu fara cin abinci fauzan ya shigo gaishe shi sukayi annah tace ina Ina kwana batare data kalleshi ba,  ya amsa batare da shima yakalli inda take ba
    fitowar momy yasa kowa ya fara cin abinci dankali ne da doya sukayi tare da soup din kaza, abinci yayi ma fauzan dadi sosai,  ya kalli ummi yace ummi wayayi wannan breakfast din? tace yayah annah da leemas sukayi
    leemas tace a'a nidai doya kawai nasoya annah ce tayi dankali da soup,  sai lokacin ya d'aga kai ya kalleta aikam suka had'a ido,  wani yar annah taji har cikin kafarta
    Dauke kai tayi shima ya share kamar bai ganta ba, bayan sungama breakfast suna falo zaune fauzan yace momy akwai abokina da mukayi karatu a can London  yanaso yazo katsina wurina,  zaiyi two days sannan ya tafi yau zaizo
   Momy tace toh shikenan allah ya kawoshi lafiya,  fauzan sunyi waya da abdulmajeed kan cewa ya iso yazo ya tafi dashi,  ba karamin dadi fauzan yaji ba
    Already dama anma abokin abinci 12:30 fauzan ya shigo gida shida abdulmajeed,  momy ta tarbeshi sosai su ummi ma sukafito aka gaisa,  annah ce tafito falon abdul majeed na kallanta yace *matawalle* da sauri annah ta d'ago kai tace yah majeed, mikewa yayi tare da cewa matawalle meya akawo ki nan?ina dad da mom?
    da gudu ta rungumeshi tana kuka, sai da leemas ta riketa ta bata hakuri, majeed ya samu labarin duk abinda ya faru da annah ya kuma tausaya mata, nan ne annah ke tambayarshi ina zee take?? majeed yace annah zee na gida da taso tabiyoni wai ta sauka wurinki
    Annah tace ya majeed bani number ta,  bata yayi tasa a phone dinta mikewa tayi tanufi ciki anan ne majeed ke gayama fauzan inda ya san annah
    annah dai neighbour dinsu ce sadda suna katsina,  koda yaushe annah na gidansu wurin zee dan har suka saba anzama yan'uwa, bakaramin kuka annah tayi ba lokacin dasu majeed zasu tashi su koma bauchi, ummi tace toh ya majeed naji ka kirata da matawalle? Yace eh matawalle suna wani boyfriend  din da annah ta ta'bayi ne
   tun daga lokacin duk wanda yasanta yake kiranta da matawalle,  dan inba gidansu ba ba inda aka ce mata annah,  awaje kam kowa matawalle dan idan zaki shekara kina tambaya annah  a mkrnt baza'a gane ba sai kince matawalle
    Deejah tace tab lallai kunsan juna,  ranar kaf annah natare da majeed dan koda yaje sallah la'asar ya dawo suna tare, sai da momy takirta sannan tatafi
   Dakin fauzan ya wuce anan ne fauzan ke cewa nikam bama wurina kazo ba wurin budurwaka kazo"majeed yace wacece budurwata matawalle wai kake nufi? Yace eh
     majeed yace haba matawalle kanwatace amma ni zan rokeka wani abu idan zakamin?  Yace insha allahu idan har ina da dama zan maka"majeed yace sonike ka auri matawalle
     fauzan yace what annah sbd me zan aureta, majeed yace sbd annah nada duk abinda kakeso jikin mace, ka kalli matawalle kuwa sosai kaga ga fari ga hanci idanu dara dara masu kyau,cike kirjinta yake da dukiyar fulani ga hali ba abinda annah tarasa kai da kakesan mace me dan karamin baki gata kasamu me kuma kake nema?
  Fauzan yace kai malam why not kai bazaka aureta ba tunda tana da kyau ni sai kamin tayi, majeed yace ni inajin kunyar kallan annah ince insanta, tamkar kanwa take  a wurina
   Fauzan yace kai kasan son da nakewa safiya kuwa, hotanta fauzan ya nuna ma majeed tare da cewa kaga wadda zan aura, majeed ya kwashe da dariya tare da nuna pic din safiya yace yanzu wannan ce zaka aura? Fauzan yace eh me ita wadda kakesan in aura tafita dashi?
       majeed yace tafita kyau kaga tafita idanu ita farace ga dukiyar fulani ga hashi hanci kai wannan bama zata had'u da matawalle ba, fauzan yace kai kawani dameni da dukiyar fulani ina ruwana da wannan ni abinda ya kwanta mani nike magana ba surar jiki ba, majeed yace habawa fauzan ka mance kata'ba gayamin kai ko aure zakayi kafison me dukiyar fulani sosai,  sai yanzu ne zakace kai bawannan ba

DIDECATED TO YOU *Asmie b aliyu*💋💋💋💋💋


Maryerm mukhtar👅👅👅👅👅👅👅

Love you all my fans
[01/07, 12:03 a.m.] ‪+234 706 571 7620‬: 🔆💜🔆               🔆💜🔆
     🔆                           🔆
   *NIDA YAH FAUZAN*
🔆💙🔆                 🔆💙🔆
     🔆                             🔆


*Episode 21-25*

Love you my group members
*MARYERM MUKHTAR HAUSA NOVELS GROUPS*📚📖📘✍🏼

✍🏼Writeen by
*Maryerm Mukhtar*

Annah tace wacece safiya kuma? Leemas tace safiya itace wadda yah fauzan keso dan har neman aure anje rana kawai ake jira afidda, annah tasake mai maita sunan safiya
   Leemas tace yadai annah kodai kodai, annah tace kodai me wlh bawani abu sai da suka gyera komi suka goge ko ina sannan suka fita
     da daddaren ranar momy tace gobe kowa karfe 9:00 zai tashi daga bacci sbd za'ayi abinci kala kala saboda bakon da zaizo, ranar annah dakin su leemas ta kwana ummi kuma takoma dakin deejah
    Haka kuma akayi karfe 9:00 suka tashi abinci anyi kala kala wajen kala goma akayi bayan sun gama komi annah taje tayi wanka tasa wani red lace gata fara sai tayi wani irin kyau kamar diyar roba
    Tasa plat takalmi red ummi da deejah wani kallo suka bita dashi sbd su kansu sunsan tayi kyau,leemas ma tayi kwalliya sosai kuma duk sunyi kyau
     Wajen 11:00 suna zaune falo akayi hon momy tace kuje kuga kowaye a waje,mikewa sukayi su duka suka fita wata motace tashigo black dan ba'aganin kowaye cikin mota tsayawa sukayi suna jiran suga waye cikinta
      Bude motar akayi d'aga kan dazasuyi sukaga fauzan na masu murmushi da gudu suka ruga suka rungumeshi suna dariya kowace murna takeyi sosai
    ita dai annah tsayawa tayi tana kallansu sbd yanda taga kyawun fauzan yafi najikin pic, sun kusa minti5 ahaka sannan Leemas tace welcome back yah fauzan,  yace tnx my dear
    Inafata nasameku lfy"tace alhamdulilah ciki suka nufa Ta gefan annah fauzan ya ratsa ya wuce dan ko kallanta baiyi ba
     tsoki tayi tawuce ciki itama yana shiga falon ya rungume momy kowa ranar murna yake cikin gidan, momy tace toh kunga suprise din dana ke gaya maku koh? Ummi tace lallai momy babban suprise kuwa
     fauzan yace yanzu dai nagaji bari inje inyi wanka sai muzo muyita fira, momy tace yawwa jekayi dama abincin ka na nan najiranka
     daki ya wuce yana shiga ya aje phone dinshi kan gado ya shiga toilet yayi wanka ya fito ya dan shafa mai kadan ya sharce gashin kanshi yasa black kaya ya nufo cikin gida
      Yana shigowa ummi tai mashi iso zuwa dinning fauzan yace dame dame kukq dafa mani ne? Ummi tace abubuwan da kakeso mana bude marfin kulolin tayi idanshi ya fad'a kan alkubus da miya
    fauzan ya rud'e tare da cewa wow my foverite food ummi miko mani alkubus din nan ranar yacishi sosai sai da ya gama yasha kunun aya mai dadin gaske
    falo ya dawo ya zauna ya kalli leemas yace leemas sarkin aiki gsky alkubus dinnan yayi dadi kin kara iya girki sosai
    leemas tace yayah bani nayi ba annah ce tayi,  yace wacece annah kuma?? momy tayi mashi bayani komi ya tausaya mata, leemas tace in kirta ne? Yace a'a kyaleta sunsha labari ranar ana kiran sallah azahar ya tafi massalaci
      annah na cikin sallah leemas tashigo bayan tasalame ne leemas ke bata labarin yanda fauzan ya yaba abincinta, annah ta tsinci kanta cikin murna da batasan dalilinta ba
     da la'asar leemas taja annah suka tafi garden labari sukeyi sosai anan ne annah ke cewa leemas ita da sadda tana gida banda karatun english novel ba abinda takeyi sbd batada abokin labari
    leemas tace kamar yah fauzan kenan shima yana san karanta novel,  dan kam har wurin aje books gareshi
      Annah tace dan allah ko zaki samomin wani in karanta? Leemas tace ok bari idan ya shigo ciki falo ya zauna ana labari nikuma zan shiga in dauko maki yanda bazai ganni ba
    Annah tace toh sai lokacin leemas ke cewa annah wai bakida waya ne? Annah tace ina da waya tana cikin jikkata tun sadda mum da dady suka rasu na kasheta na daina amfani da ita
    Ammah zansa ta charge yau da daddare ana kiran sallah suka shiga ciki bayan sunyi sallah ne annah tafito falo tasa phone dinta charge,ciki takoma deejah nafitowa taga waya a charge ta kalli ummi tace iphone din waye wannan kodai ta yah fauzan ce
    Muryar leemas sukaji tana cewa ta annah ce charge tasa, ba karamin mamaki sukayi ba ganin annah narike manya wayoyi, leemas ta nuno masu ipad din dake hannuta tace wannan ma tatace charge zansa mata
     Wucesu tayi tasa charge sannan ta dawo ta zauna,  momy ma falo tafito fauzan yazo ya zauna suna labari,  annah ce tafito rike da laptop a hannu tanufi inda tasa charging wayoyinta ta cire iphone din tasa laptop dinta
    bayan tashiga ciki ne fauzan ke cewa momy wannan  wai wayoyin waye tare da laptop? Leemas tace na annah ne
       yace wai ita wannan yarinyar bata fitowa wane bare aganta asaba tunda nazo banganta ba


*DIDECATED TO YOU asmie b aliyu*💋💋💋💋💋


Maryerm mukhtar👅👅👅👅👅👅👅


Love you all my fans
[01/07, 12:03 a.m.] ‪+234 706 571 7620‬: 👅💋💋Ya🔆💜🔆               🔆💜🔆
     🔆                          🔆
  *NIDA YAH FAUZAN*
🔆💙🔆                🔆💙🔆
      🔆                          🔆


*Episode 31-35*

*MARYERM MUKHTAR HAUSA NOVELS GROUPS*📚📖📘✍🏼


✍🏼Written by
Maryerm mukhtar


Fauzan yace kai kyaleni nidai kanwar taka batai min ba,  nikasan ba komi kemin ba kuma ma da kake cewa annah ina ni ina karamar yarinya idan auren kauye akamin na haifeta,16years fa gareta haba barima wannan maganar kaji,
    Haka sukaita surutansu da daddare suna zaune falo anata fira majeed yasa aka kira mashi annah tana fitowa  fauzan ya d'aga kai yana kallanta gani yayi duk abinda abokinshi ya lissafa annah na dashi ba karya yayi ba, ganin kallan da fauzan ke mata yasa duk ta tsargu
    Da kyar ta ida isowa ta zauna majeed keta janta da fira,  amma kam shi fauzan da sun had'a ido sai ya dauke kai, annah duk tabi ta damu cikin ranta tace me wannan mutumin yake kallo a jikina, ranar sai da majeed yasa annah tasaki jiki
      annah batasan kallo ta tsani taga namji na mata kallan kuri, sai tabi ta daure fuska haushin fauzan taitaji ranar ana gama fira tamike tashiga ciki,  washe gari da safe suna yin breakfast leemas kece mata annah jiya ni naga yah fauzan namaki wani kallo kodai yana ciki ne,  annah tace hmm leemas kenan wane irin yana ciki
     aini halin yayanki bemin ba ko kadan yana da matsala ya cika miskilanci da yawa,  leemas tace kai annah kinga kam kun dace dan wlh idan kika auri yah fauzan kin sami miji dan duk mace tanasan namji kyakyawa kuma mai halin kirki
      annah tace ke nidai kyaleni ina da matawallena da nakeso a hannu kuma shi zan aura in allah ya yadda, leemas tace bana ce ameen ba tundani yayana nakema kamu,  haka suna aiki suna fira har suka gama,
       ranar annah sanye take da lace brown ya mata kyau riga da skirt, suna zaune falo suna cin abinci fauzan da majeed suka shigo annah da fara'a tace yah majeed ina kwana"yace lafiya qlau matawalle ci gaba da cin abincinta tayi batare data gaida fauzan ba,
     Mamaki ya kamashi sbd me taki gaidashi,cikin ranshi yace lallai yarinyar nan bata da kunya sai na gyara mata zama
    Sukayi breakfast suka gama falo suka dawo suka zauna, majeed yace fauzan ya kamata mu dan fita da la'asar yau mana tare dasu,fauzan yace muduka wai? Majeed yace eh mu daje wani joint muci abinci
       ummi ta yawwa yah majeed soli center zamuje muci shawarma da pizza, majeed yace dama na dade banzo katsina ba dan haka yawo zamuyi cikin garinnan  koh matawalle? Annah tace eh ye majeed
      Fauzan kam haushin annah ya kamashi sbd ya lura rainashi takesan yi,  duk zamannan da akayi falo  harara annah kawai fauzan yake,kuma ta lura da sun had'a ido take gallamashi harara
     Da la'asar annah tasa green tamfa mai manya fulawoyi tamata kyau sosai tasa black takalmi heels dan ko gyele batasa ba,  fitowa tayi waje nan tasami kowa ya fito ita yake jira,  wani mugun kallo fauzan yai mata ganin ko gyele batasa ba,  ya bude baki zaiyi magana  yaga sauran ma suma basusa gyelan ba,  dole yayi shiru
      fauzan yayi driving din nan suka wuce soli center kowa yaci abinda yakeso, anan ne fauzan ya lura favorite  dinshi d'aya da annah dan duk abu iri d'aya sukaci
     harda pics sukayi amma idan fauzan na hannu dama toh annah annu hago zata koma,  majeed yasa su dole sukayi pic tare su biyu
      anan ne majeed da leemas suka kara ganin yanda suka dace, majeed sai da yasa aka biya wurin hoto  ya biya kudi a wanke mashi na annah da fauzan
    Sai gab magriba suka koma gida dan ko abinci dare basuci ba, a ranar ne su ummi sukaita rokon majeed yayi masu 5days annah ma tasa baki dole majeed ya hakura sbd annah
     Washe gari ne mai pic ya kawo hotan daya wanke babbane sosai, idan ka gansu a pic din sai kace mata da mijine sbd kyan da sukayi, momy da dady da sauran yan gidan na zaune majeed ya shigo da pic din,  kowa sai da ya fadi kyan da pic din yayi
   Dan kam ita momy sai da tayima danta sha'awar auren annah,  dady kam murnashi sai data bayyana
     Fauzan kasa magana yayi sbd haushin ganin pic din, leemas ce ta anshi pic din tasa a falo kusa dana fauzan
    Hotan sai ya haske falon dan daka shigo dashi zakayi tozali, mikewa fauzan yayi ya fita,  annah ma tamike tashiga ciki✍🏼


DIDECATED TO YOU *Asmie b aliyu*


Maryerm mukhtar👅👅👅👅👅👅👅👅


Love you all my fans
[01/07, 12:03 a.m.] ‪+234 706 571 7620‬: Ya🔆💜🔆               🔆💜🔆
     🔆                          🔆
  *NIDA YAH FAUZAN*
🔆💙🔆                🔆💙🔆
      🔆                          🔆


*Episode 36-40*

*MARYERM MUKHTAR HAUSA NOVELS GROUPS*📚📖📘✍🏼


✍🏼Written by
Maryerm mukhtar

Nakine wannan page din *khaleesat hydar* allah ya bar kauna yar'uwa😍


Dady yace akwai wani abu tsakanin yarannan ne?? leemas tace a'a dady bakomi tsakaninsu amma gsky dady ni zanso a had'asu aure dady wlh da yayah ya samu mata annah kuma tasamu miji, momy tace gsky ne da kau anrike amana da aka bamu,  mu aura da annah ga danmu da mukasani
    Dady yace a'a tunda babu wani abu tsakaninsu a kyalesu,  tunda kinga har aure naje kaduna na tambayar mashi,  karmu zama kanana mutane, sbd jiya mahaifin yarinyar ya kirani yake sanar dani sun fidda rana 2 month sukasa sai mukai kayan sa biki
    Momy tace toh shikenan idan annah matar fauzan ce zai aureta,  yanzu yaushe za'akai kayan sa bikin? dady yace gobe  dan nasa wani abokina dake can kaduna ya sayi komi sukai gobe
      Momy tace toh allah yasa munada rabon gani, dady yace ni yanzu ma miji na fiddawa haleematu kuma ina fata zai amshi tayina, momy tace waye??  Dady yace abdulmajeed abokin fauzan, momy tace toh ka kirasu su duka kamasu magana
       haka kau akayi dady ya kira leemas da majeed cikin ikon allah majeed ya amshi tayin dady,  hakama leemas ta yadda
     *bayan kwana biyu*
Ana gobe majeed zatafi leemas duk ta canza annah zai janta take tana takwace mata yaya, har karfe 11:00 leemas da majeed suka kai suna fira,  kuma dady yayi da majeed cewa da ya koma gida zai turo iyaye asa biki so ake a had'a auren leemas da fauzan lokaci guda
      washe gari majeed ya tafi gida tunda  ya tafi kullum sai sunyi waya da majeed bayan kwana biyu iyayen majeed sukazo aka gaida iyaye akasa rana 3 month banbanci wata daya dana fauzan
      Yau takam asabar annah na kitchen fauzan ya shigo kalkanta yayi tare da cewa ke ina leemas? Annah tai banza ta kyaleshi ya sake maimaita mata
    Juyawa yaga zatayi tatafi ya jawota ya had'a da bango tare da cewa ke kin isa in maki magana ki banzatar dani,  wacece ke mikeke takama dashi
    daurewa tayi cikin rashin kunya tace dalla malam ka sakeni, fizge kanta tayi tare da nunashi da yatsa tace bari kaji na ba irin matan da suke zuwa suna banzatar da kansu ba
     Idan ka kuskura ka kara ta'bani sai kagane kuranka,  aurenka nike da zaka ta'bani koni matarka ce,  mamaki ya rufeshi da har ya tsaya wannan yarinyar tana gaya mashi magana
      Fita tayi daga kitchen din tabarshi tsaye yana tunanin irin hukuncin dazai mata,  itakam tunda takoma daki take tunanin meyasa taimashi haka bayan tasan tanaji a ranta kamar san yah fauzan take,  me yasa ta wulakanta  abinda takeso
     tarasa me yasa takejin fauzan a ranta tun ranar data fara ganin pic dinshi,  takumaji ciwo dataji ansa mashi biki da wata,  haka taita tuhumar kanta
    Fauzan kau ji yake kamar ya fasa ihu saboda takaici, tun daga ranar sai ya zama bata bari had'u ko kadan, kusan two weeks kenan basu had'u ba rannan tana goge dining table ya shigo ba karamin tsoro taji ba data ganshi,  kallanta ya tsaya yanayi ita kuma abinda ta tsana kenan namiji ya tsaya yana kallanta
    dakewa tayi tacigaba da aikinta ya matso kusa da ita yace wow yarinya ke gani kike kin isa koh,  shiyasa kike duk abinda kika ga dama
     Toh amma nasan maganinki wani Leda taga yana bud'ewa tai saurin ja da baya,  kusa da ita ya matso sai kawai gani tayi ya saki ken kyaso bisa ita,  tsalle ta daka ta d'aleshi bisa kirjinshi ta lafe
    Wani shock yaji har cikin kafarshi,  wullar da ita yayi tare da gaura mata mari kuka tasaka sosai har sai da momy taji tafito da gudu ta ruga bayanta tana kuka, kallanshi momy tayi tace me kayi mata?? ya dan shafa kai sannan yace bakomi momy,  ni ban mata komi ba
     annah tace momy kyankyaso yasa min ajiki, momy tace kaga fauzan kafita harkkata wlh wato muguntar taka har takai kasa mata kyankyaso ajiki


DIDECATED TO YOU *Asmie b aliyu*

Maryerm Mukhtar👅👅👅👅👅👅👅👅


Love you all my fans
[01/07, 12:03 a.m.] ‪+234 706 571 7620‬: Ya🔆💜🔆               🔆💜🔆
     🔆                          🔆
  *NIDA YAH FAUZAN*
🔆💙🔆                🔆💙🔆
      🔆                          🔆


*Episode 41-45*

*MARYERM MUKHTAR HAUSA NOVELS GROUPS*📚📖📘✍🏼


✍🏼Written by
Maryerm mukhtar

Fauzan yace yah hakuri momy bansa ranki zai 'baci bane, juyawa momy tayi tashiga ciki annah kuma ta wuce daki tana shiga ta fad'a kan gado tan ajiyar zuciya, leemas tace ya dai annah lafiya kike ajiyar zuciya? annah tace yayanki ne mana
    Leemas tace me kuma yayi nasan dai baya shiga lamarinki, annah tace hmm toh bari kiji kyankyaso ya samin ajiki, wlh nakusa suma leemas nufashina har daukewa yayi aikam yana samin na daka tsalle,annah sai tayi shiru bata ida ba
    leemas tace ina jinki kika daka tsalle kikayi me? Annah tace awuce wurin kawai amma gsky ya cutar dani"leemas tayi dariya tace allah ya sawake dai, tun daga ranar fauzan bai kara shiga harkarta ba,  ko shigowa yayi ya ganta baya kulata, idan tana wuri tashi yake yi haka idan yana wuri tashi yake, fauzan ya zama ko cikin gida ta daina shigowa  ya zama wani miskili,ya daina zama ayi labari dashi, kullum momy cikin fad'a take mashi sbd tasan me yasa ya daina shigowa,
   *yau takama saura kwana goma bikin fauzan da safiya* kowa murna yake gidan anata shirye shiryen biki,  fauzan sai zarya yake daga katsina zuwa kd, ana cikin wannan ruguntsumin ne annah, deejah,ummi suka sami admission universty din *al 'kalam* dady ne yace ita leemas a can bauchi inda zata zauna aka ne man mata makaranta,
Anfara shagalin biki, ana gobe kunshi dady yasa aka kaisu kd,annah taso a barta gida, ammah dady yace A'a taje momy ce takarama annah karfin gwiwar zuwa biki, dan ita annah kosan ganin safiya bataso,ranar talata akayi kunshi annah batasan dalilin da yasa safiya ke mata wani mugun kallo ba
     Fauzan kam ranar kamu kamar ya shake annah sbd haushinta da yake ji, karfe 6:00 na marece aka tashi kamu,  nan leemas tace su tafi gida tau sbd gobe za'a kai amarya katsina,  tasan momy na bukatarsu kusa
     haka kam suka dauki hanya ana kiran sallar magriba,  basu iso ba sai karfe 10:00 suka tadda gidan ciki yake da mutane"momy tayi mamakin ganinsu cikin daren nan
     annah suna isa daki tashiga ta fad'a toilet wanka tayi tafito tasa kayan bacci, phone dinta ta dauka tashiga instergram pics din safiya da fauzan taga anata watsawa,  batasan sadda ta jefar da wayar ba ta fashe da kuka
     leemas ce tashigo tana tambayar ta lafiya? Annah tayi saurin share hawayenta tare sa cewa bakomi,  ranar annah batayi bacci ba,  tarasa me yasa data runtse ido take ganin fauzan ba
      haka har gari ya waye anata shirye shirye, sai ranar annah tasan cewa fauzan wata d'aya kawai zasuyi garinnan ammah abuja zata zauna,
karfe 12:00 aka tafi daurin aure,  aurin cike yake da mutane kowa murna yake, baban amarya dana ango tsaye suke tare suna gaisawa,wani dan saurayi ne ya taho inda suke daka ganshi kasan mai hankali ne, gaidasi yayi suka amsa, ya kalli dady yace alhaji kai kake rikon annah? Dady yace eh
       Saurayin yace................  Hankalin dady ya tashi ya rasa me zaiyi akan abinda aka gaya mashi, baban amaryar yace kaga dai yarinyar nan amana ce wurinka mafita kawai ka had'a fauzan da annah,  ni na yarda  ya auri su duka biyun
    Dady yaji dadi sosai fauzan besan me ake ciki ba ko kadan, aka daura auren safiya da fauzan, mutane har zasu fara tafiya akace su dakata za'asake daura wani auren,  fauzan yayi mamakin auren wa za'a daura, baban safiya ya wakilci iyayen annah, kuma shi ya bada aurenta, jiyayi ance an daura auren fauzan da rukayya,  wani tashin hankali yaji, dan baima gane wa ake nufi ba
   
DIDECATED  TO YOU *Asmie b aliyu*


Maryerm Mukhtar👅👅👅👅👅👅👅👅👅👅👅👅


Love you all my fans
[01/07, 12:03 a.m.] ‪+234 706 571 7620‬: 🔆💜🔆               🔆💜🔆
     🔆                          🔆
  *NIDA YAH FAUZAN*
🔆💙🔆                🔆💙🔆
      🔆                          🔆


*Episode 46-50*

*MARYERM MUKHTAR FANS GROUPS*📚📖📘✍🏼

Writeen by Maryerm Mukhtar

*sorry sisters wlh bana jin dadi ne shiyasa banyi typing ba kuyi hakuri*👏🏼👏🏼👏🏼


Mikewa yayi ya nufi mahaifinshi yace dady nida wace aka daurama aure? Dady ya kalleshi yace annah"fauzan yace annah kuma dady me yasa aka daura min aure da ita? wuceshi dady yayi batare da ya bashi amsa ba, mota fauzan ya nufa yana shiga da karfi ya buga marfin motar, har zai tada dady ya kirashi awaya yace ya jirashi yanaso zasuyi magana,kusan 1hour fauzan najiran dady takaici ya kara kamashi musamman idan ya tuna wacece annah da abinda ke tsakaninsu' dady ya gani tsaye ta glass din motar budewa fauzan yayi ya fito,  dukawa yayi kanshi kasa dady yace ya mike
    kallon fauzan dady yayi yace fauzan nasan kayi mamakin meyasa na daura maka aure da annah, fauzan inaso kayi biyayya da abinda zan fadi maka, fauzan kasan annah amance gareni dan haka inaso ka riketa da amana dan allah fauzan banaso in gaya maka dalilin aurenku ammah aurenka da annah kamar taimakonta daga masifar data tunkarota ne, fauzan ina mai baka umarni da karka saki ka cutar da annah idan kayi abinda zai cutar da ita banyafe maka ba, karka banbanta ta da safiya duk matanka ne
    Sundade suna magana daga bisani sukatafi, katsina suka nufa fauzan duk bai cikin farin ciki,  basu isa ba sai wajen 4:00 lokacin ne aka taho da amarya katsina
      tunda su fauzan suka koma gida ya shige d'aki ya rufe,annah kam sunata aikin walimar gobe,dady yai ma dady momy bayanin komi da kuma dalilin had'a auren,  hankalin momy ya tashi takuma ji dadin hukunci da dady ya yanke
     Ankawo amarya aka kaita part din da dady ya basu su zauna kafin sutafi,  mutane suka cika gidan sai lokacin fauzan ya shigo cikin gida, Annah nashiri shiga kitchen rike take da plates din abinci fauzan yai sallama,  jitayi gabanta ya fadi tad'ago kai suka had'a ido dauke kai yayi kamar ma bai ganta ba, ya nufi dakin momy
  Hakuri momy takara bashi kuma tasake gaya mashi karya saki ya cutar da annah, sun dade suna magana, har lokacin ba wanda yayi ma annah bayanin komi
    Momy ta sanar dasu leemas komi inda leemas taita tunanin taya yah fauzan zai zauna da annah bayan kiyayyar dake tsakaninsu,  leemas ta dade da sanin annah nasan fauzan sai dai bata nuna mata tasani ba
     Annah ta lura da leemas na boye mata wani abu amma sai ta share,
  *washe gari* tunda safe su annah sukayi wanka riga da skirt tasa lace din yellow ne yayi mata kyau sosai, duk anko sukayi
Su annah nata had'a ma amare breakfast a kitchen angama had'a komi momy tasa masu aiki suka dauki kulolin tace annah tabisu akai,

Annah nafita ta hango fauzan tsaye jikin mota cikin wata farar shadda tayi mashi kyau sosai, wani farin ciki ya lullu'be annah,  daurewa tayi tashiga cikin gidan, amare zazzaune a falon sunata fira, annah ta danyi masu sannu tace ga breakfast dinsku
    Ajewa masu aikin sukayi annah d'aga kan dazatayi sukayi ido hud'u da safiya dake tahowa daga daki, sauri annah tayi zata juya safiya tace jimana, annah ta juyo safiya tace kece annah? tace eh nice
    safiya tai murmushi tace good zaki iya tafiya, fitowa annah tayi tare da mamakin me yasa take tambayarta,  tafiya taci gaba dayi dan ko gabanta bata gani, karo taji sunyi da wani tai saurin yin baya
      d'ago ido tayi sukai ido biyu da fauzan,  annah ta daure tace ya hakuri dan allah"fauzan yace is ok
   Kiringa kula idan kina tafiya, wuceta yayi mamaki ya kamata me yasa fauzan ya canza gaba d'aya,  haka taita tunanin iri-iri
    Wajen 10:00 mutane sai kara zuwa sukeyi,docoretion din garden din gidan akayi yayi kyau sosai
    wurin ya zama kamar za'ayi party,  kafin kace me wajen 12:00 wurin ya cika da mutane sosai
  Safiya red dress tasa tayi kyau sosai, kawayenta ne suka shigo da ita filin,  daga baya ne ango ya shigo shida abokanshi
   pictures kawai ake masu,  karfe 4:00 mutane suka fara regewa zuwa 6:00 gidan ya zama saura kadan,amarya na zaune falo zaune itada su deejah annah tashigo safiya tawani watsa mata harara, annah kam tarama
      Zama annah tayi ta fiddo phone dinta tana dannawa, safiya kam ranta duk ya 'baci kiran da momy tai mata ne  yasa tamike tashiga cikin dakin, daga bisani aka kira safiya da fauzan zama sukayi kowa yayi shiru dady ya fara da cewa annah na yanke wani hukunci da ban sanar dake ba,  kuma inaso duk abinda zan gaya maki zakibi umarnina annah jitayi gabanta na fad'uwa gawata kyarma data kamata,  da kyar tace ina jinka dady
    Dady yace yau wajen daurin auren safiya da fauzan kema na had'aki aure da fauzan, annah tace dady kamar yah? Yace ina nufin an daura aurenki da fauzan
     annah tai saurin mikewa tsaye tace sbd me dady??  yace sbd ina da dalilina nayin haka
*basu ankara ba sai dai sukaji karar fad'uwar annah yaraf ta suma*😭😭😭😭


DIDECATED TO YOU *Asmie b aliyu*


Maryerm mukhtar👅👅👅👅👅👅👅👅👅

Love you all my fans
[01/07, 12:03 a.m.] ‪+234 706 571 7620‬: 🔆💜🔆               🔆💜🔆
     🔆                          🔆
  *NIDA YAH FAUZAN*
🔆💙🔆                🔆💙🔆
      🔆                          🔆


*Episode 51-55*

*MARYERM MUKHTAR FANS GROUPS*📚📖📘✍🏼


✍🏼Written by
Maryerm mukhtar

*Ga Barka da sallah dina sisters*

Allah ya maimaita mana allah ya karbi ibadunmu


Da sauri momy ta dauketa ta tasata bisa kujera,  ruwa aka yayyafa mata ta farfad'o kuka tasaka da kyar momy ta lallasheta dady ne yace abar maganar yanzu tunda abin na niyyar 'baci, mikewa annah tayi tatafi daki tana kuka
    Safiya kam takaici ya kamata banda rainin wayau irin na yarinyar nan ta auri mijinta kuma ta dawo tana wani kuka muna finci, dady ya karayi masu nasiha akan su zauna lafiya
 Part dinsu suka tafi suna shiga safiya ta daure fuska cikin fushi tace fauzan haka mukayi da kai? dama mu biyu ka shirya aure? fauzan yace ba haka bane saf(safiya) wallahi bansa dalilin da yasa aka aura min ita ba, saf kinsan ke kadai nikeso duk duniya,  bawata diya mace da zanso bayan ke
    Rungume juna sukayi ita kam can annah ranar ko bacci takasa, cikin ranta take cewa shin farin ciki nakeyi ko bakin ciki, annah tarasa meke damunta yau gashi abinda take mafarki yazo gareta ammah tarasa mike damunta miye matsalarta,
*Washe gari*
Wajen. 10:00 gidan ya zama tsit bakowa leemas ita da annah sukayi share share da goge goge, daki annah takoma tayi wanka tasa riga da skirt ba atamfa tayi kyau sosai, kin fitowa tayi falo kowa na zaune falo, momy tafito tace leemas ina annah? leemas tace momy tana daki bacci take wai kanta ke ciwo"momy tace toh shikenan suna cikin magana safiya da fauzan suka shigo har kasa suka duka suna gaishe da momy, cikin fara'a momy ta amsa"deejah tace yaya dama ku muke jira muyi breakfast, zama sukayi kan dinning leemas tamike ta nufi daki annah ta samu zaune tayi tagumi, leemas tace annah momy tace kizo muyi breakfast, mikewa tayi sukafito fauzan ta hango ya juya baya ta dauke kanta, tana zuwa taja kujera suka zauna ba wanda ya kalli kowa safiya ta kalli annah ta watsa mata harara,annah kam ta rama tare da daure fuska
    Tunda annah ta zauna ko kallon inda fauzan  yake batayi ba,tazuba abinci tanaci kowa ya gama annah tamike ita da leemas suka kwashe kayan
   Falo suka dawo suna kallo.phone din annah tayi ringing tamike tashiga ciiki wajen 12:00  annah suka shiga kitchen ita leemas suna abinci fauzan ya shigo ya kalli leemas yace kidafa mana raliya da miyar albasa nida safiya
   Leemas tace yayah ni fita zanyi kasan nafara hidima annah zan bari tacigaba dayi,fauzan ya kalli annah ya kauda kai ya fita.annah tadafa macroni da miya tajera komi kan dining
    muryar safiya da fauzan taji a bayanta suna dariya.tajuyo fauzan ya kalleta yace kin dafa taliyar??annah tace kasani in dafa ne??yayi mata wani kallon mamaki yace amma kinji ina fadima leemas tace fita zatayi meyasa ke bakiyi ba
   Annah tace sbd bakace annah ta dafa maka taliya ba,juyawa tayi ta wucesu safiya tawani 'bata rai tare da juyawa tatafi itama


DIDECATED TO YOU *Asmie b aliyu*


Maryerm Mukhtar👅👅👅👅👅👅👅👅


Love you all my fans
[01/07, 12:03 a.m.] ‪+234 706 571 7620‬: 🔆💜🔆       🔆💜🔆
     🔆                   🔆
*NIDA YAH FAUZAN*
🔆💙🔆        🔆💙🔆
    🔆                     🔆


Episode 56\60


*Maryerm Mukhtar Fans Groups📚📖📘✍🏼


✍🏼Writeen by
Maryerm Mukhtar

©MIKIYA WRITERS ASSOCIATION✍🏼

Fauzan ya tsaya yana mamakin annah cikin ranshi yace haka zamuyi rayuwar da ita,cikin raini da rashin girmamawa fauzan ya fadi afili yace dole nagayawa dady dan bazan bari karamar yarinya ta rainani ba wlh dan ko safiya da nakeso ban bari ta rai nani ba bare ita
   Komawa yayi ya lallashi safiyqa da kyar ta hakura,bayan kwana✌momy taje kasuwa aka hadoma annah lefe kamar yadda akayiwa safiya,momy taba kawarta kudi tasiyo min bags da shoes a england,an ma annah akwatuna masu yawa da kayan makeup dady ya fiddo hundred thousand ya ba annah kudin sadakinta, washe gari leemas ta raka annah ta dinku nanta wurin tailor sbd gab suke da tafiya abuja, ana haka akayi bikin leemas da majeed.annah tasha kemewarta bayan kwana 3 da gama biki  ana zaune falo da daddare fauzan ke cewa momy nan da 4day nakeso mutafi sbd asibitin suna bukatata kusa.momy tace toh shikenan kasan gobe za'aje ayima annah jere can gidan naku,zansa akara sharewa sbd kura tunda gab kuke da zuwa koh
   Ran safiya ya baci cikin ranta tace wato gida 1zamu zauna tare da wannan yarinyar tab wlh bazan yarda ba,shigowar annah ya dawo da safiya.momy tace annah ina kikaje da daddaren nan?annah tace momy Auwal ne yazo mugaisa"momy tace wane auwal?tace jikan matawallen katsina ne na dade da saninshi"momy tace toh shikenan jeki
  Annah tashiga ciki inda ta fada kan gado tana kuka.tunowa da abinda matawalle  ya gaya mata
  Cikin kuka annah takira leemas take ce mata leemas nashiga uku auwal yazo gidannan wai ya dawo da soyayyata,bakiga kukan da yayi ba sadda yasan an dauramin aure leemas naso auwal amma yanzu ba yadda zanyi sbd lokaci ya kuremin
    Leemas tace annah kiyi hakuri allah zai fiddo maki mafita amma inaso in sanar dake cewa inma kinsani inma baka sani ba kina son yah fauzan wlh kina mashi so mai karfin gaske annah
   Tun ranar da kika fara ganin pic dinshi na lura da feelings dinki,annah kidaina bama kanji wahala kifita ki nunawa yah fauzan kina sanshi Ku fahimci juna
     Annah tace zan Iya amsa maki cewa ina son yah fauzan amma annah bazan Iya gaya mashi ba,bansan meyasa nake mashi rashin kunya ba duk sadda ya min mgn,leemas tace annah kidai kiyaye kinga yah fauzan matsayin mjinki ne bai kamata kina irin haka ba Nan dai leemas tayi ma annah fada sosai
     washe gari da safe annah na zaune falo fauzan ya shigo sanye da blue shadda sai kamshi yake daurewa annah tayi tace ina kwana!ba yabo ba fallasa ya amsa mata
  Da la'asar auwal yazo wurinta suna tsaye jikin mota fauzan ya fito daga part dinsu sanye da bakin jeans da farar riga.daga nesa ta hangoshi tafara murmushi da dariya fauzan yazo ya gitta ko kallansu beyi ba
     sai da tagama tashigo zata gitta ta wuce fauzan ya kirta batare data jiyo ba ta amsa,fauzan yace waye wannan yazo wurinki?annah tace friend dina ne akwai wani abu ne?fauzan yace ke karaki rainawa mutane hankali ya zaki ringa wasa da mutane da aurenki zaki fita gaban kato kina wasu dariya da murmushi
   Kinsan abinda kikeyi kuwa kodan kinga bana kulaki yanzu inda tarewa kikayi zaki kai minshi cikin gidane?annah tace dakata malam ya zaka zauna kana min fada toh dan an auramin kai sai akace kasamin ido.yawwa kuma bari makaji kajawa matarka kunne tafita har kata dan ta girmemin nesa bakusa ba
   Fauzan kamar ya daura mata mari ammah ya kyaleta sbd kar ran momy ya 'baci,da daddare fauzan ya gayawa dady abinda annah taimashi, dady yayi ma annah fad'a sosai ya kuma karamasu fada
   Washe gari annah ta shirya cikin afterdress black tayi kyau sosai karfe 6:00 suka dauki hanya.cikin mota safiya da fauzan sukaita kabari da wasu darairaku fauzan ya dago kai ta glass yana kallon annah yaga phone take amfani da ita
   karfe 1:00 suka isa unguwar maitama suka isa wani babban gida aka bude masu suka shiga gidan tamkar unguwa guda parking space sukayi parking kowa ya fito masu aiki suka shiga da kayan ciki.fauzan yayi gaba suka bishi baya
      Wani babban falo suka shiga fauzan ya kalli safiya yace ga part dinki 3room 2bedrooms, ya kalli annah yace ga naki part din 3bedrooms 2falo.wannan kuma falon da muke ciiki nakowa ne ni nasayi komi na ciiki
  Annah ta nufi part dinta daya daga ciikin  dakin da aka nuna mata tashiga,dakin gaba daya kayan cikin duka farare ne bag dinta da gyele tacire tashiga toilet tayi wanka tafito tasa yar karamar riga mara nauyi ta kwanta
    Bata tashi ba sai 4:00 tayi sallah tayi wanka tasa riga da skirt na atamfa yellow tayi mata kyau sosai,mai aiki ce tashigo rike da leda a hannu.tace aunty ga abinci inji maigidan yace akawo maki!annah tace owk kawo ta ansa kadan annah taci ta aje a gefan gado


DIDECATED TO YOU *ASMIE B ALIYU*


MARYERM MUKHTAR👅👅👅👅👅👅👅👅👅👅👅
 


Love you all my fans
[01/07, 12:03 a.m.] ‪+234 706 571 7620‬: 🔆💜🔆.          🔆💜🔆
     🔆.                      🔆
 *NIDA YAH FAUZAN*
🔆💙🔆.         🔆💙🔆
     🔆.                    🔆


Episode 61/65


Maryerm Mukhtar F✍🏼ans Groups📚📖📘


Written by Maryerm Mukhtar✍🏼

©MIKIYA WRITERS ASSOCIATION✍🏼


Yarinyar data kawo mata abinci ce ta dawo tace aunty wai kizo falo alhaji na kiranki!annah tace Owk ina zuwa.mikewa tayi ta sauko kasa inda taga fauzan zaune shida Safiya,annah ta zauna tare da cewa gani
    fauzan yace mgn ce zamuyi game da rabon kwana,dan banasan rigima musamman ke annah bakyajin mgn ko kadan,kuma kamar yadda kika sani anyi aurena dake bisa wani dalilin da bansanshi ba!kema kuma bakisanshi ba
   Toh dan haka ni ban daukeki matsayin matata ba! na daukeki matsayin kanwata toh kinga ba wani dalilin Rabin kwana da azayi,safiya dai itace matata kuma it's nakeso dan haka banso kizo kina mata rashin kunya ko rashin mutunci
   Zaki tsaya amatsayin kanwata a yanzu amma kika nan gaba idan kika ida cika mace sosai Sai muga abinda za'ayi,annah tace kamar ya bangane ba so kake kaceni ban cika mace ba komi,da kasan da haka meyasa baka gayawa dady cewa ni bancika mace ba!kuma ko yanzu ai bata 'baci ba zaka Iya sakina
  Kuma kafin kace infita saga harkar Safiya kafara gayamata tafita harkata nima dan bazan sauki wulaqanci ba,kuma ni gidannan ai ban bukaci abani matsayin mata ba na dauki zuwana garinan tamkar nazo karatu dana gama zan koma
     Fauzan ya daka mata tsawa sai da ta razana,zaro ido yayi tare da cewa ke how dare you ni zaki gayama baki bukace abaki matsayin mata ba!ke kin isa ki gayamin abinda zanyi wacece ke
   Toh bari kiji kisan abinda kikeyi ni ba tsaranki bane juyawa yayi ya fita safiya tamike tace ke wait rayuwarki bakida mutunci ko kadan, baki Iya komi ba sai rashin kunya toh bari kiji duk rashin kunyarki sai in fidda maki ita
   Annah ta watsa mata kallo tare da cewa koh!nizaki fiddama rashin kunya hmm toh karki fara wannan kuskuran da like shirinyi
  Annah tamike tashiga ciki,da daddare bayan sunyi sallah tafito falo ta tadda fauzan da safiya na cin abinci ko kallansu batayi ba,tawuce kitchen ta bude frizer taga bakomi cikinta tafito ta hau sama ta dauko kudi tanufi waje
  Fauzan baice mata komi ba taje ta dawo falo ta zauna,safiya tace kalli sbd girman kai bazata Iya cewa ina abincinta ba tawani share!fauzan yace kyaleta ai wuya makaranta kare zata nemi abinci da kanta
  Suka gamaci suka dawo falo suma labari suke sosai yaron gidan ya shigo dauke da Leda annah tamike ta ansa bayan yaron ya fita tamike zata tafi daki fauzan yace ke miye wannan??tace lemu da cake lafiya??yace ke kinfi karfin ki tambayi ina abincinki wato shine kikaje kika bada asawo maki!annah tace ai nasan kasiyo min sbd naga abinda kukeci nasan nima shine shiyasa ban tambaya ba sbd bana cin abinci mai nauyi da daddare
     Fauzan yace matsalarki ce jeki annah ta juyo tace matsalar kanwa ai tamkar matsalar kace sbd ni kanwace wurin ka kamar yadda kace ya kamata abani kulawa kamar yadda aka ba sauran kanne
  Juyawa tayi tahau sama fauzan yace wannan yarinyar sai shegiyar bakar magana wlh sai nayi maganinta,washe gari wajen 10:00 annah ta tashi tayi wanka tasa riga da skirt na lace red tayi matukar kyau
  Tafito falo ta yadda fauzan sanye cikin white shadda sai kamshi yake yana danna laptop,annah taje gab dashi tamkar zata danneshi tace ina kwana!dagowa yayi yana kallanta tare da bayyanar mamaki a fuskarshi yace lfy qlau danne ni zakiyi ne?tace A'a me kagani ya watsa mata kallon banxa yace dama idan zaki gaida mutum haka kikeyi
   Tafadi tare da turo baki Tace yanzu gaisuwar ma ya zama laifi toh shikenan daga bazan sake gaisheka ba!yace ke nikike turoma baki zan bige bakin wlh,mikewa yayi ya nufi dakin safiya inda yaga har yanzu bacci take gashi tun da asuba yake tadata tayi sallah amma taki,gashi har kwanciyar aure sukayi amma ko jikinta bata gyera ba
   Kara tada yayi ta kalleshi tace kai sweetheart kana da matsala baka barin mutum yayi bacci wlh,fauzan yace safiya ko wanka bakiyi ba ga sallah asuba ma bakiyi ba!safiya tace zanyi idan natashi mana rufe kanta tayi da bargo taci gaba da baccinta
   Fauzan ya sakko kasa inda yaga annah zaune tana waya sai lokacin yaga irin kyan datayi gashi sai kamshi take,duk duniya fauzan ba abinda ya tsana irin rashin kula da rashin sanyin ibada ya kuma lura safiya duk tana dasu,wuce annah yayi ya fita bai dawo ba sai 11:00 ya siyo kaya masu yawa lemu kala kala da ice cream ya shigo da kaji buhu  guda akasa a frizer da cake kala kala
   Dakin safiya ya nufa sai lokacin yaji karar ruwa ake waye,ya jira tafito daure da towel kallanta yayi tare da cewa kinyi sallah??tace a'a yanzu zanyi bakaga yanzu nafito bane
    Yace yanzu dan Allah haka ya dace?ace sallar safe sai 11 zakiyi ta ina ma amfani,nan tazo tana ban hakuri da lallashi yana zaune ta shirya taxa doguwar riga na Atamfa suka fito falo tare Suna fara'a nan be fauzan ke gaya mata gobe zai fara zuwa asibiti Aiki nan taimashi Allah yasa alkhairi
   Tace sweetheart yunwa nakeji ba'ayi breakfast bane??fauzan yace a'a bansa kowa yayi ba sbd ni banacin abincin masu Aiki ki gida su leemas kemin abinci,kafin su Iya kuma momy keyi
  Safiya tace tab toh yanzu ya zamuyi gashi nikuma yunwa nakeji!fauzan yace nima banci komi ba yanzu kije ki dafa mana ko ruwan zafi ne kisoya kwai muci da bread!safiya tace kai dear yazan Iya yin wannan duk aikin kallifa jiya yanda kabani wuya wlh da kyar nake motsi,ya watsa mata harara yace ke wai toh ni zan mana aikin komi??


DIDECATED TO YOU *Asmie b Aliyu*


MARYERM MUKHTAR👅👅👅👅👅👅👅👅👅👅


Love you all my fans
[01/07, 12:04 a.m.] ‪+234 706 571 7620‬: 🔆💜🔆.          🔆💜🔆
     🔆.                      🔆
 *NIDA YAH FAUZAN*
🔆💙🔆.         🔆💙🔆
     🔆.                    🔆


Episode 66/70


Maryerm Mukhtar Fans Groups📚📖📘


Written by Maryerm Mukhtar✍🏼

©MIKIYA WRITERS ASSOCIATION✍🏼


Tace no ba haka nake nufi ba toh why not annah bazata yi mana breakfast ba,fauzan yace ke annah ce zatayi mana breakfast ke miye aikinki look safiya kije ki dafa ruwan zafi ki soyamin kwai ina jiranki a dining,har zaitafi ya dawo yace yawwa kiyi tare da annah sbd banaso aringa raba abinci agidannan
  Safiya ranta ya baci tanufi kitchen ta bude frizer ta dauko kwai 7 tafasa uku wuri daban tasake fasa 4wuri daya,ta dora ruwan zafi duk ta kone wurinyi,tasoya kwan ta dauko tafito inda taga fauzan yana waya.ta aje kan dining taje ta dauko bread ta dauko cups ta kawo surger da lipton ta aje,cikin cika da batsewa tace gashi amma fa sweetheart duk na kone wlh kallifa!fauzan yace sannu sweety
  Annah ce tadoso wurin inda taja kujera ta zauna kallan safiya tayi tace ya dai matar yayana?cikin fushi tace ina ruwanki dani!annah tace sorry matar yaya nikam yunwa nakeji bari in faraci
    Annah ta yanki bread ta dauki kwai tasa tsakiya ta hada tea dinta ci daya tayi tamike da gudu sai daki,fauzan ya kalli safiya yace meya tada wace ne??safiya tace nima bansani ba
  Fauzan ya dauka zaici yaji muryar annah tana cewa wait wlh karkaci gishiri yayi yawa gashi ko albasa batasa ba karnin kwai din yana nan
   Fauzan ya watsa mata kallon banza ya dauka yaci,ci daya yayi ya mike da gudu sai daki safiya ta ciri kwan taci taji gishir tamkar tasa buhu guda
  Annah ta kwashe da dariya tare da cewa allah sarki matar yaya,bansan baki iya girki ba ai danazo nayi maki!safiya ta daga hannu tamari annah,wani irin zafi taji aikam annah tadaga tamareta daidai fauzan ya sakko daga steps,tsawa ya dakama annah inda ya iso ya kalleta tare da cewa how dare you zaki daga hannu ki mari safiya!annah ta kalleshi tare da cewa baka tambayeta abinda taimin ba sai kafaramin fada
  Aikam fauzan ya shareta da mari,kuka tasaki tare da tafiya sama da gudu,fauzan ya kalli safiya yace sorry sweety wannan yarinyar batajin mgn kiyi hakuri!safiya tace bakomi amma gsky kasake jamata kunne karta sake kuskuren marina idan ba haka ba zan rama wlh
  Fauzan yace shikenan yanzu je dauko gyelanki muje restaurant muci abinci!tace toh sama ta shiga ta dauko gyele sukafita
   sukayi breakfast dinsu waje nan na fauzan yace bari ya sawoma annah nata itama afita hakkinta,safiya bataso ba amma munafurci baisa tanuna mashi ba. Sai ta nuna tanaso asawo
   Aikam suka dawo annah na daki fauzan ya shiga tana kwance kan gado tayi shiru ya kalleta ya jefa mata ledan abinci yace gashi nan idan zakici
   Harya juya zaitafi tace dakata malam ni ba karya bace dazaka jefomin abinci,bana ma bukatar abincin da kasiyo min dan kosan ganinka banayi"mikewa tayi tace fauzan idan cutar dani zakayi meyasa baka sakini ba tun kafin muzo nan?idan kiyayyar da kakemin takai haka meyasa zaka rabani da inda nakejin dadi
    Wlh fauzan nayi nadamar biyoka da nasan haka zakamin da ban yarda da zama matarka ba,rike hannu yayi tare da cewa idan kin gaji zaki iya tafiya dan ni bana bukatar zamanki gidannan kin takuramin nida matata
   Kuma abinci idan bazakici ba ke kika sani!fita yayi daga dakin annah tasake fashewa da kuka tare da cewa zuciya meyasa zakiso wanda bai sanki?meyasa zaki kaunaci wanda baya tunaninki
  Zuciya bakiyi min adalci ba idan kika barini naci gaba da san fauzan,tai kuka sosai daga bisani ta hakura nan bacci ya dauketa da kyar tayi sallar azahar takoma bacci
  Da la'asar annah tasa red jeans da farar riga ta bala'in yi kyau ta daure kanta tasa red takalmi tafito falo safiya da fauzan na zaune ta wuce kitchen ta dauko lemu tanufi hanyar fita waje
   Fauzan ya kira sunanta bata amsa ba sai dai kawai tsayawa datayi,yace ina zaki da wannan shigar??tace gardin zanje kanada sako ne?yace haka zakije gardin din gida cike da maza
  Annah tajuyo da manyan idanuta tace Ooh toh nida ba aure gareni ba ai gara inje in nemi miji cikinsu ko allah yasa na dace
  kaifa yaya nane kaga kau bai kamata ka hanani zuwa neman miji ba,juyawa tayi tafita fauzan kam ranshi ya 'baci safiya tace kayi hakuri sweetheart kasan yarinya ce kuma batajin mgn sai dai kawai muyi mata addu'a(Makira☺)fauzan yace gsky kina da zuciya mai kyau sweety kallifa abinda tayi maki amma ke sassauci kike neman mata!safiya tace bakomi ai tamkar kanwace a wurina


DIDECATED TO YOU Asmie b aliyu

Maryerm Mukhtar👅👅👅👅👅👅👅👅👅👅


Love you all my fans
[01/07, 12:04 a.m.] ‪+234 706 571 7620‬: 🔆💜🔆.          🔆💜🔆
     🔆.                      🔆
 *NIDA YAH FAUZAN*
🔆💙🔆.         🔆💙🔆
     🔆.                    🔆


Episode 71/75


Maryerm Mukhtar F✍🏼ans Groups📚📖📘


Written by Maryerm Mukhtar✍🏼

©MIKIYA WRITERS ASSOCIATION✍🏼


Fauzan yace shiyasa nakesanki sweety rungumeta yayi ita kam zuciyarta kamar ta fashe sbd takaicin annah,mikewa safiya tayi tashiga kitchen tana dafa abinci dare.ita kam  tunda annah tafita bata shigo ba sai gab magriba tana shigowa ta hadu da fauzan nashirin fita zuwa masallaci ko kallanshi batai ba ta wuce
   Bayan sunyi sallah ne suka nufi dining table suka zauna safiya sai kyarma take sbd tana gudin allah yasa abinci yayi dadi,isowar annah ta dawo da ita daga duniyar tunanin daya tafi da ita,annah ta zauna safiya ta zubama fauzan tasama kanta wani mugun kallo taima annah tare da cewa bari insa maki ko kanwata,fauzan na dago kai tafara murmushin munafirci
   Ya kalli annah yaga fuskarta daure"yace ma safiya kyaleta tasa da kanta ke baiwarta ce!annah tazuba dan kadan taliya jalop ce
  Har fauzan ya kai baki zaici aka kirashi awaya,nan ya aje yana wayar annah tayi spoon guda da kyar ta cinyeshi tayi wurgi da spoon din kasa tare da zuba ruwa a cup tanasha,fauzan ya gama wayar ya kalli annah wadda gaba dayanta zufa take yace ke miye zaki jefar da spoon din
  Annah tace sbd naga kasheni akesanyi a gidannan! Ya za'aringa bani abunci da zai cutar dani??fauzan yace idan kika kara wata mgn zan tsinkeki da mari
  Shiru tayi yayi  spoon daya da sauri ya debi ruwa yasha ya kalli safiya da jikinta duk ya mutu yace sweety miye wannan ya zakiyi abinci kin cika gishiri ga yaji yayi yawa!safiya tace ya hakuri sweetheart wlh nayi iya kokarina dan inga yayi dadi nakasa
  Fauzan ya mike ya fita daga gidan.annah tashiga kitchen ta dauko indomie ta dafa taci,nan aka bar safiya zaune tana takaicin abinda ya faru da ita,fauzan bai dawo ba sai 10:00 lokacin har safiya tayi bacci amma ya hango fitilar dakin annah a kunne take
*Washe gari*
  Fauzan yayi wanka tunda asuba wajen 7 ya fito falo ya shiga kitchen ya dafa ruwan zafi ya soya kwai  yasha tea ya fita duk abinnan da ake safiya bacci take kawai
  annah ta tashi 10:00 tayi wanka tasa kaya kitchen tashiga ta dafa indomie ta kwai taci ta koma can falonta nasama ta kunna zeeworld tana kallon  twist of fate, safiya bata tashi ba sai 12:00 tafito falo taga bakowa phone dinta ta dauka takira fauzan inda yake cewa shifa yana wurin aiki
  Safiya ma tarasa yanda zatayi ga yunwa tanaji tashiga kitchen din tadafa indomie tazo tana faraci taji kamar tai amai aikam ta aje tashiga ciki ta dauko kudi tabada aka siyo mata breakfast, time din ne annah tafito ta tadda safiya zaune falo tawuce ta kitchen tashiga ta dauko freshmilk da cake tanaci matsayin abinci rana
    Da la'asar tayi wanka tasa dan karamin skirt pink💕 iya kaurinta ya tsaya tasa white riga ta matseta sosai ta gyera gashin kanta tasa pink shoe👡 plat tafito falo ta wuce kitchen kaza tafido ta yanki kwata  ta wanketa ta gyera ta fiddo vegetables suma ta gyerasu,ta dafa cus-cus jalop gidan ya dume da kamshin abinci safiya tarasa ne wannan yarinyar take dafawa haka gida ya dume da kamshi haka
  Ana kiran sallah magriba ta sauke abinci dama dan kadan ta dafa tazuba a plate ta rufe tanufi daki taje tayi sallah,fauzan ya shigo agajiye ya shiga daki yayi wanka safiya duk tana can kitchen tana juye abinci data bada akasawo mata a restaurent a kula bataso fauzan ya gane ba ita tayi ba
    fauzan ya fito falo ya nufi dining sbd shi tunaninshi kamshin da yaji gidan nayi na abinci toh maybe ta gyera abinci yace sweety har kin gama girkin??tayi dan murmushi tace eh sweetheart bakaji kamshi na tashi bane?yace ai tunda nashigo naji kamshi shiyasa har kyarma nake nafito
  Ya zauna safiya ta zubamashi abinci dai dai nan annah taxo ta dauko abincinta ta zauna tafaraci,nan fauzan yaga abinci ba iri daya bane kuma abinci da takeci shike kamshin da yaji ya bude gidan
  Ya dago kai yace annah ina kika samu wannan abinci??annah tace dafawa nayi akwai wani abune??yace what to meyasa kinga sweety na dafawa kema kika dafa bayan kinsan nace banso ana raba abinci?annah tace sbd bazan iya zama kullum ace abinci restaurent zanci ba!fauzan yace kamar ya??tace kamar yadda tabada kudi aka sawo mata Abinci a restaurent takawo maka a matsayin ita ta dafa!ya dago ido yana kallan safiya tai sauri taja baya


DIDECATED TO YOU *Asmie b Aliyu*



Maryerm Mukhtar👅👅👅👅👅👅👅👅👅👅

[01/07, 9:33 a.m.] ‪+234 706 571 7620‬: 🔆💜🔆.          🔆💜🔆
     🔆.                      🔆
 *NIDA YAH FAUZAN*
🔆💙🔆.         🔆💙🔆
     🔆.                    🔆


Episode 76/80


Maryerm Mukhtar Fans Groups📚📖📘


Written by Maryerm Mukhtar✍🏼

©MIKIYA WRITERS ASSOCIATION✍🏼


Yace sweety da gaske siyowa kikayi??ta daure fuska tace ya zansiyo abinci ni nadafa wlh karya take!annah tace baiwar allah basai kin rantse ba ban fadi dan ya yarda ba nafadi abinda nasani ne kawai
  Annah tamike zata tafi ya jawota ya hada da bango tare da cewa ke miyesa ba kyajin kunyar kimin rashin kunya??annah da tsoro ya cika mata zuciya ta daure tace niba rashin kunya nayi maka ba kawai dai nasan ba lallai ka yadda dani bane shiyasa
  Ya murde mata hannu tare da matsowa da ita gab dashi suna shakar numfashin juna yace ke wlh sai nayi maganinki,annah da gaba daya jikinta ya mutu sbd irin kallan da fauzan yake yi mata
  Idanushi sukayi mata kwarjini jitake aranta dama karya saketa sbd yanda jikinsu ya hadu da juna"wani kallan kauna take mashi sai da taji ya wurgar da ita tadawo hankalinta
   Mikewa tayi tanufi daki inda shima ya koma kan dining yana cin abinci,tunda annah takoma daki take tuno halin data shiga sadda fauzan ya danneta jikin bango ji take zuciyarta kamar zata fito sbd bugawa
  Tafadi afili tace dama fauzan zaiji abinda naji a yanzu dama fauzan zai soni kamar yadda nake sanshi,gaba daya sha'awar fauzan ta lullu'be annah sbd idan ta tuno sadda ya hadata da bango kirjinshi sai da ya fito waje
  Mikewa tayi tashiga toilet tayi wankan sallah tafito tayi sallar isha'i gaba dayan daren annah mafarkin fauzan ta kwana tanayi, washe gari ya fita office tunda safe Yinin ranar annah tana dan gudun haduwa da fauzan take sbd bataso ya fahimci wani abu daga wurinta
    Da daddare suna falo zaune tafito zata shiga kitchen fauzan yace yawwa annah kishirya gobe zan kaiki universty din dana neman maki  admission ya fito,annah tace toh
    Tunda asuba annah tayi wanka tasa riga da skirt na atamfa red tayi kyau sosai tasa red gyele da red takalmi👠 tasa red bag👜 karfe 6:50 dai dai tashirya tafito falo ta zauna shiru fauzan bai fito ba,mikewa tayi tanufi dakin safiya tayi knocking shiru ba'a bude ba.ta tura kofar safiya tagani kwance tana bacci da alama fauzan banan ya kwana ba
    Tanufi dakinshi ta tura karar ruwa taji da alama wanka yake ta nemi bakin gado ta zauna, fauzan ya fito daure da towel a kugunshi mikewa tayi tace dama najika shiru shine nazo in gani ko ka shirya
   Kallanta yayi sama da kasa yace shine sai kin shigomin har daki?juyawa tayi zata tafi sul'bin kasa ya jata tayi baya baya zata fadi fauzan ya rikota tafada kan kirjinshi aikam shima sul'bi ya jashi suka fada kan gado baki dayansu
   Dagowa tayi tana kallanshi sukayi ido biyu ta kalli bisa kirjinshi take har yanzu tai saurin mikewa daga bisashi,d"an hannu dan' hannuta ya makele jikin towel din dake jikinshi
  Nan annah ta rude tai tai tacire takasa,taja hannu aikam towel ya kwance daga jikin fauzan,ihu tasaka tamike da sauri zata fita fauzan ya jawota ta dawo bisa shi
   Ya zaro mata manya idanushi tare da cewa ke dama abinda ya kawoki nan dakin kenan!ke har kinyi girman da zaki bukaci d'a namiji har zaki biyoni daki koh
  Wato kin kawo kanki??annah da kirjinta kamar zaifito sbd bugawa tace yah hakuri wlh kiranka nazoyi,ya jefar da ita daga bisa kanshi ya mike ya jawo towel din har sai da dan hannuta ya kare yaji mata ciwo
  Ya daura towel din ya shafa mai yasa kaya ya feshe jikinshi da turare duk tana nan kwance tana kuka,yasa takalmi ya kalleta yace kitashi mutafi idan bahaka ba zantafi in barki,Fita yayi daga dakin annah tamike tasa takalminta ta goge hawayenta tafita zaune tasamu fauzan a mota
  Tashiga ta zauna tana shashekar kuka'fauzan ya kalleta yace idan kuka zakiyi fitarmin daga mota
  Aikam annah tayi shiru ya fizgi motar suka fita


DIDECATED TO YOU *Asmie b aliyu*


Maryerm Mukhtar👅👅👅👅👅👅👅👅👅👅👅👅👅


Love you all my fans
[01/07, 12:50 p.m.] ‪+234 706 571 7620‬: 🔆💜🔆.          🔆💜🔆
     🔆.                      🔆
 *NIDA YAH FAUZAN*
🔆💙🔆.         🔆💙🔆
     🔆.                    🔆


Episode 81/85


Maryerm Mukhtar F✍🏼ans Groups📚📖📘


Written by Maryerm Mukhtar✍🏼

©MIKIYA WRITERS ASSOCIATION✍🏼


Ta glass din mota ya dago ya kalleta yaga duk jikinta yayi ja alamar ta tsorata,yayi murmushin mugunta yaci gaba da tafiya sukaje suka duba sunanta ya fito daganan ya wuce da ita office dinshi parking taga sunyi ta kalleshi tace yana ga munzo hospital?? Ya watsa mata kallan banza yace sbd bazan iya maidaki gida ba shiyasa na taho dake nan
  Annah tazaro ido tace har sai katashi daga office kenan?yace eh inzaki fito kifito idan kuma nan zaki zauna shikenan!annah ta mike tafito
   Cikin asibitin suka nufa fauzan ya hado da wasu abokanshi ya gabatar da annah matsayin kanwarshi ce ,fauzan ya gayyacesu zuwa dinner gidanshi gobe
 Ciki suka shiga inda ya nufi office dinshi ya shiga saman kujera annah ta zauna fauzan yasa farar riga ya fita, har karfe 2 fauzan bai dawo ba tun fitar da yayi
  Annah tafito taga wata nurse zata wuce tace yawwa dan allah ina doctor fauzan yake ne?nurse tace doctor fauzan yana can yana duba patient tun safe da yazo kuma yanzu sun shiga operation!annah tace owk nagode
  Cikin asibitin annah take zagayawa dataga dai bazata kai karshenta ba sai tadawo office dinshi ta zauna,bacci ya dauketa kiran sallar la'asar taji tamike tashiga toilet tayi alwalla tayi sallah da gyelan jikinta
    Takoma ta zauna ga yunwa dake cinta sbd ko gida da safe bataci komi ba,knocking taji anyi tace yes wani ne yashigo kamar mai aikin goge goge a hospital din yace madam gashi doctor yace akawo maki
  Ta ansa tayi godiya abinci ne aka kawo mata nan taci abinci sosai ta bude ruwa tasha,taci gaba da zaman jiran fauzan
   Sai wajen magriba fauzan ya shigo ya cire farar rigar yace muje koh!annah da ranta ya 'baci tamike suka tafi tunda tashiga motar bawanda yace ma kowa komi.shiru ya bude motar wani restaurent suka tsaya yasiyo masu ice cream shida safiya roba biyu
  Annah dai batace mashi komi sai da ya fara tafiya tace yaya kasiyo ice cream ko kamance gida munada shi dayawa
  Fauzan da shaf ya mance yace Ooh na manta amma bakomi,gida suka shiga safiya na zaune falo tana cika tana batsewa sukayi sallama ko kallansu batayi ba bare ta amsa
   Fauzan yayi murmushi yace sweety kina falo ashe?tace eh ina nan mikewa tayi tahau sama yabi bayanta,annah da gaba daya tagaji tashiga daki tayi wanka tayi sallah magriba tafito falo taga bakowa tashiga kitchen ta dauko freshmilk tasha takoma daki tayi sallah isha'i sannan ta kwanta
  Mafarkin abinda ya faru yau da safe ta kwana tanayi bata tashi ba sai karfe 11:00 time din har fauzan ya tafi office yana can wajen 4:00 ya tuno ya gayyato friends dinshi zasuci abinci gidanshi yau da daddare aikam ya taho gida
   Safiya na zaune falo tana kallo,fauzan ya shigo safiya tace ya naga ka dawo yanzu lfy??fauzan yace wlh dai kam baki zamuyi yau da daddare zasu zo cin abincin dare
   Safiya tace toh yanzu ya zamuyi nidai ban iya abinci ba sosai!yace toh ya zamuyi safiya tace toh musiyo a restaurent mana!yace a'a badai a restaurent ba
  Safiya tace to muba luba mai aiki tayi mana!yace a'a inaso nima inci kuma ni bana cin abinci masu aiki!fauzan yace yawwa ina annah ai ta iya girki dan ko a gida tanayi duk gidanmu leemas tafi kowa iya abinci toh har leemas annah tafita iyawa
   Safiya tace wlh muddin muka bari tasan alfarmata muke nema zamusha rashin kunya!fauzan yace leemas zansa tayi mata mgn.leemas ya kira ya gaya mata tace owk bari tayi mata mgn
  Leemas takira annah tace annah dan allah abinci zakiyi abokan majeed zasuzo gaidaku toh kinga safiya bata iya komi ba,annah tace hmn ke bawani abokan fauzan ne zasu zo ai nasani
  Leemas tace toh nidai tunda kin gano ki taimaka kiyi,annah tace zanyi tunda ke kika roka bazan ce a'a ba
   leemas tace ngd sukayi bankwana,annah tafito ta kalli fauzan tace me dame za'a dafa??yace yawwa kiyi shinkafa da miya sai kiyi cus-cus da vegetables
    Ta wuce kitchen tafara aikinta fauzan yace sweety bazakije kiga yanda akeyi ba!safiya tace allah ya sawake wlh ai sai ta rainani fauzan yace shikenan
  Wajen magriba tagama komi taje tayi sallah tayi wanka ta canza kaya doguwar riga tamfa tasa already har friends din nashi sunzo safiya tafito suka zazzauna
  Safiya ta zazzuba masu abinci karar sakkowa anna tasa suka dago da kansu kowa ita yake tayi wani masifar kyau ga kamshin turaren da takeyi  kujera taja ta zauna ta gaishesu suka amsa cikin fara'a usman ne yace kanwarmu irin wannan kwalliya haka!tayi murmushi
  Fauzan da gaba daya ranshi 'bace yake sbd yanda annah take ta labari da usman suka gama usman yace wai wayayi abincin nan annah tace aunty safiya ce!suka fiddo kudi suka ba safiya,annah kam usman ya bata da zasu tafi ya amshi no dinta tabashi


DIDECATED TO YOU *Asmie b aliyu*


Maryerm  Mukhtar👅👅👅👅👅👅👅👅👅👅👅👅👅👅👅



Love you all my fans
[01/07, 11:32 p.m.] ‪+234 706 571 7620‬: 🔆💜🔆.          🔆💜🔆
     🔆.                      🔆
 *NIDA YAH FAUZAN*
🔆💙🔆.         🔆💙🔆
     🔆.                    🔆


Episode 86/90


Maryerm Mukhtar F✍🏼ans Groups📚📖📘


Written by Maryerm Mukhtar✍🏼

©MIKIYA WRITERS ASSOCIATION✍🏼



Fauzan ya dawo daga rakasu yaga annah tabar falon ya bita daki zaune ya taddata kan gado yace ke wai mikike nufi??tace banga ne ba kamar ya?yace owk baki gane ba koh belt taga yana cirewa taruga tashige toilet fauzan yace ki bude toilet dinnan yaji tayi shiru dole ya fita
  Dataji kamar bakowa tafito tai sauri ta kullo kofar dakin, ranar fauzan kwana yayi yana tunanin irin hukuncin da zaima annah
  ************
Washe gari
Fauzan kafin ya tafi office   ya nufi dakin annah yaji rufe dole ya tafi aiki,da la'asar annah tayi wanka tasa brown dress tayi matukar kyau phone dinta tayi ringing ta dauka muryar wani saurayi taji
   Tace wake mgn?aka usman ne abokin yayanki!tace yawwa ina yini ya gida??yace lfy qlau!ya fara da cewa annah dama abinda yasa na amshi number ki dan in sanar dake abinda ke raina!annah tace kafin ka gayamin inaso zan dan baka wani labari
  Yace ina jinki tace wata yarinya ce budurwa takamu da san wani saurayi tun kafin yayi aure,tafara sanshi lokacin da taga pic dinshi a gidansu amma da aka bata labarin halayenshi sai ya dan fara bata haushi! amma steal tana jin sanshi a ranta kullum kara sanshi takeyi. Duk fa abinnan da ake basu ta'ba haduwa ba! amma sai taji  labarin cewa yana da wadda zai aura
   Har anje ne man mashi aurenta daga ranar sai yarinyar tafara shiga damuwa gashi iyayenta sun mutu gidan su yaron take zaune
   Rannan sai akace zai dawo daga kasar waje ya gama karatunshi na doctor,da ya dawo sai taji san da takemashi a yanzu yafi nada duk abinda zaiyi burgeta yake
   Amma sai ta lura yana da girmankai yan mata da dama sun soshi,tunda ya dawo gidan bai taba yima yarinyar mgn ba gashi ita kuma tamutu kanshi
   Sai kuma allah yasa mashi tsanar wannan yarinya dake sanshi,ya takura mata idan yana wuri bata zama idan tana wuri baya zama
  A haka har akasa ranar shi dawata wadda yakeso amma yarinyar bata daina sanshi ba!toh ranar daurin aurensu da amaryarshi sai aka daura mashi aure da yarinyar da ke sanshi da wadda yakeso duka aka aura mashi
   Bayan sun tare sai ya kirasu su duka yace ma yarinyar dake sanshi cewa ita baifa dauketa a matsayin mata ba ya dauketa tamkar kanwarshi,dan haka bai taba zuwa dakin yarinyar ba duk wani hakkin aure na tarayya mace da namiji bata ta'ba had'asu ba kuma bai ta'ba sanin tana sanshi ba
   Annah ta nisa sannan tace me kake gani ya dace taci gaba da sanshi har tayi winning heart dinshi ko kuwa??usman yace bai kamata ta barshi ba har sai tayi winning heart dinshi, annah tace kasan wacece na baka labarinta kuwa??yace a'a
  Tace toh labari na nabaka *Nida Yah Fauzan*usman yace dan allah da gaske ne ko wasa??tace wlh da gaske ya faru
   Usman ya nisa sannan yace annah ya zama dole kiyi winning heart din fauzan,na tausaya maki sosai dan duk macan dakesan namiji shine bayasanta abin akwai wahala
    Annah tace ngd usman daka fahimce ni amma inaso kayi min wani taimako guda,inaso ka ringa kirana dan fauzan ya dauka soyayya muke sbd inaso inga koda kishina ne fauzan yana yi           ***********
Usman yace insha allah zan taimaka miki annah sukayi bankwana ta kashe wayarta
   Da daddare suna zaune falo phone din annah tayi kara ta dauka tana murmushi tare da cewa hello usman, zuciyar fauzan kamar tafashe sbd takaici sai da tagama wayar ya kalleta yace dawa kike waya??annah tace da usman abokinka!fauzan yace miye hujjarki na waya da samari ko bakisan kinada aure bane?annah tace aure kuma ka dauramin aure da wani ne yah fauzan??yace Ooh tambaya ta kike
   Tace toh aini nasan ni kanwar kace ba mata ba,fauzan yace zanyi maganinki
    ana haka har time din fara zuwan su annah mkrnt yayi,suna zaune a falo fauzan yace annah ki hada kayanki gobe zan kaiki mkrnt hostel zaki zauna!annah tace gsky ya fauzan bazan zauna hostel ba
  Ya watsa mata kallan banza yace wlh saikin zauna dan ni bazaki zo kimin zaune cikin gida ba,kin takuramin nida matata
   Bakin annah ya kubce tace yanzu idan natafi zanbar ganinka fa,yace so what dan kinbar ganina an gaya maki ni san ganinki nakeyi
  Wannan mgn taba annah haushi cikin ranta tace wato kwata kwata har yanzu baya tunani na
   Daki tatafi ranar ko baccin kirki batayi ba sbd tunanin yanda zata bar fauzan,da safe tafito da kayanta yaje ya kaita
   Tunda taje dakin hostel din take kuka wata doguwar yarinya ce tashigo dakin ta matso inda take tace baiwar allah lfy kike kuka
   Annah ta share hawayenta tace bakomi ina kewar gida ne,yarinyar tace kiyi hakuri zaki saba nima bakuwace yau nafara zuwa,sunana bilkisu ana cemin bily
  Wannan dakin ne aka kawoni,annah tace nikuma sunana rukayya amma ana kirana da annah
   Bily tace naga dakin na mutum hudu ne ina sauran suke?annah tace inaga basu zoba Bily tace mizaki  karanta??annah tace Biochemistry Bily tace nima shi zan karanta suna cikin labari wasu yan mata biyu suka shigo sanye da after dress suka gaisa daya sunanta hafsat amma lolo ake ce mata dayar kuma Aziza amma ziza aka ce mata du kansu abu daya zasu karanta


DIDECATED TO YOU *Asmie b Aliyu*


Maryerm Mukhtar✍🏼👅👅👅👅👅👅👅👅👅👅👅


Love you all my fans
Love you all my fans</i>

1 Comments

Post a Comment
Previous Post Next Post